Showing posts with label tsaro. Show all posts
Showing posts with label tsaro. Show all posts

Sunday

Amurka ta kai wa Iran hari, ta lalata musu makaman yaki

Wasu rahotanni daga Amurka sun bayyana cewa kasar ta kai wani hari ta yanar gizo (internet) a kan kwamfutocin da dakarun soji na juyin-juya hali a kasar Iran ke amfani da su wajen sarrafa manyan makaman yaki da suka hada da makamai masu linzami (nukiliya).

Rahotanninsun bayyana cewa an ai harin ne a ranar Alhamis bayan shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya canja ra'ayinsa a kan kai hare-hare a wasu wurare mallakin kasar Iran.

Harin da Amurkan ta kai ba zai rasa nasaba da harbo wani jirgin yakin kasar Amurka mai amfani da na'ura da kasar Iran ta yi ba a cikin makon jiya da kuma wani harin da aka kai wa jiragen dakon danyen man fetur na Amurka, wanda ta dora alhakin kai harin a kan kasar Iran.

Babu wata kafar watsa labarai wacce ba ta Amurka ba da ta bayar da tabbacin cewa harin ya lalata makaman yakin kasar Ira.
Shugaba Trump dai ya bayyana cewa kasar Iran ta tafka babban kuskure da ta harbo jirgin yakin kasar Amurka da ake sarrafa wa da na'ura.

Jirgin, maras matuki, da Iran ta harbo na daga cikin jiragen yaki masu matukar tsada da kasar Amurka ta mallaka.

DUBA WANNAN: Yadda 'yan sanda suka yi wa wasu masu garkuwa da mutane dirar mikiya a mafakarsu. ðŸ”—

Trump ya bayyana cewa zai shafe kasar Iran daga doron kasa idan yaki za su yi.
Wutar yaki da ke ruruwa tsakanin kasashen biyu ta jawo zaman dar-dar a kasashen yankin Persia.

Tuni Andrew Murrison, sakataren harkokin kasashen waje na kasar Birtaniya ya isa kasar Iran domin tatauna wa da shugabannin kasar domin yi musu sulhu da kasar Amurka.

Shugaba Trump ya bayyana cewar a shirue yake ya yi sulhu da kasar Iran tare da bayyana cewar kasar Amurka a shirye take idan kasar Iran yaki take so su gwabza. Sai dai, ya gargadi kasar Iran da ta sani cewa Amurka ba tsarar ta ba ce.

POSTED BY LEGIT.NG

DUBA WANNAN KUMA.

Yadda Ake Dawo da Lambar WhatsApp Idan ta Daina Aiki

Yadda zaku maida lambar wayar ku zuwa ta kasashen waje. in 5min

Yadda Zaku Bude Facebook Account Ba Tare Da Suna Ba.

Yanda Zaka Samu Rancen Kudi Har N100,000 A Layin Etisalat New(9mobile)  

Yadda Ake Connecting Na Android Xender Da Computer. : Android Tutorial 2020. 

Ko kuma Ku ziyarci Page namu mai tâken YADDA AKE....🔗🔗

Yadda 'yan sanda suka yi wa wasu masu garkuwa da mutane dirar mikiya a mafakarsu.

Rundunar 'Yan sandan Jihar Neja ta gano wasu gidaje da masu garkuwa da mutane don karbar kudin fansa suke amfani da su a matsayin mafaka a jihar. The Nation ta tabbatar da cewa an gano uku daga cikin gidajen a unguwar Bosso da ke Minna sakamakon bayyanan sirri da mazauna unguwar suka bawa bawa 'yan sanda. Tuni dai 'yan sandan sun rufe gidajen.

Majiyar Legit.ng ta gano cewa an kama mutane bakwai da wasu bindigu kirar AK 47 yayin da 'yan sandan suka kai sumame a gidajen. A halin yanzu 'yan sandan ba su bayar da cikaken bayani kan abinda ke faruwa ba.

DUBA WANNAN: Yanzu Yanzu: Jirgin sama ya kwace ya shiga jeji yayin sauka a Fatakwal ; Hotuna   

A yayin da aka tuntube shi, Mai magana da yawun 'Yan sandan jihar, Abubakar Muhammad ya ce baya gari saboda haka ba zai iya bayar da wani bayannai ingantattu kan gidajen da aka gano ba. Ya kuma ce duk wani bayani da aka bayar a yanzu kan gidajen zai iya kawo cikas ga binciken duba da cewa ba a kammala binciken ba.

Kakakin 'yan sandan ya ce zai bawa manema labarai cikaken bayani da zarar an kammala binciken. Kwamishinan 'Yan sandan jihar, Adamu Usman ya shaidawa wasu manema labarai cewa suna kawo tangarda ga binciken inda ya gargadi su da zuwa kusa da gidajen. Sai dai makwabta gidajen da ke aka rufe sun tabbatar da cewa 'yan sanda sun kai sumame gidan kuma an kama wani adadin mutane.

SOURCE LEGIT.NG

Monday

Daga dawowarsa : Buhari ya yi jawabi kan harkan tsaro

Bayan dawowarsa shugaba Buhari ya zanta da manema labarai da suka so jin ta bakinsa akan yawan garkuwa da mutane, fashi da makami, yan bindiga da harin ta’addanci a kasar.

Sai dai, a lokacin da ya tsaya domin basu amsar wasu daga cikin tambayoyinsu, musamman wadanda suka nuna damuwa kan kafa sabuwar majalisarsa, Buhari yace, “Ba zan fada maku ba.”

Sai dai kuma, bayan yaki amsa sauran tambayoyin, an nemi ya amsa tambaya kan yawan sace-sacen mutane a kasar, amma sai yace “na lura mukaddashin sufeto janar na yan sanda, Mohammed Adamu ya rairaye, koda dai wannan alamu ne nacewa yana aiki sosai."

KU KARANTA KUMA: Yadda farashin kayan masarufi suka kasance yayin da ake gab da shiga watan Azumi.  

Shugaba Buhari ya samu tarba daga shugaban ma’aikatansa, Abba Kyari, ministan birnin tarayya, Muhammed Bello; shugaban hafsan soji, Tukur Buratai, mukaddashin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Ibrahim Magu da wasu hadimansa.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa, Fadar shugaban kasa ta bukaci 'yan adawa da masu hamayya da gwamnatin tarayya da su janye kalamansu da suka yaudari wasu 'yan Najeriya da shi a kan cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ziyarci kasar Ingila ne domin a duba lafiyar sa.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dawo gida Najeriya bayan wata ziyara ta 'kashin kan sa' da ya kai zuwa kasar Ingila.

SOURCE LEGIT.NG

Hotuna : Shugaban Sojin sama ya nishadantar da Sojoji dake yaki da Boko Haram

Babban hafsan rundunar mayakan Sojan sama, Air Marshal Saddique Abubakar ya shirya ma zaratan dakarun Sojin saman Najeriya dake fafatawa a filin daga na jahar Borno, liyafar cin abinci tare da nishadantar dasu.

Sadiqque ya shirya wannan liyafar ce a ranar Litinin, 22 ga watan Afrilu a garin Maidugurin jahar Borno, inda aka ci abinci mai rai da lafiya tare da nama iya nama, aka kuma sha kayan shaye shaye da tande tande, sa’annan aka nishadantu da dadadan wakokin bare bari.

KU KARANTA: Kwana Casa'in Kashi Na 3 : AREWA24 Channel.   

Legit.ng ta ruwaito kaakakin rundunar Sojan sama, Ibikunle Daramola ne ya bayyana haka a ranar Litinin, inda yace Saddique na amfani da damar irin wannan liyafa don ganawa da dakarun Sojinsa a duk lokacin da ake wani sha’anin biki, don haka ya shirya musu wannan saboda bikin Easter da kiristoci ke yi.

Kaakakin ya kara da cewa Saddique na amfani da wannan dama don gode ma Sojojinsa, tare da jinjina musu bisa kokarin da suke yi wajen yaki da ta’addanci a yankin Arewa maso gabas, sa’annan yace irin wanna taro na dauke ma Sojojin kewar rashin iyalansu a kusa.

Babban hafsan Sojan sama ya nishadantar da Sojojin dake yaki da Boko Haram
Haka zalika baya ga Sojojin da suka halarci liyafar, rundunar ta gayyaci al’umma unguwar Gomari, unguwar da sansanon rundunar Sojan sama take zuwa wannan liyafa, inda kuma dayawansu suka amsa kira, suka ci, suka sha, suka yi nak!.

Daga karshe kaakaki Daramola yace rundunar ta gudanar da irin wannan liyafar cin abinci a sansaninta dake Yola, da kuma sansaninta dake jahar Katsina.

SOURCE LEGIT.NG

Friday

Hattara! : "Yan ta'addar jihar zamfara sun fara kaura suna shiga wasu jahohi.

A ranar Alhamis dinnan ne da ta gabata, gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola, ya bukaci jami'an tsaro da sarakunan gargajiya da su lura sannan kuma su dakile duk wani shiri na 'yan ta'addar jihar Zamfara, wadanda suke yin kaura daga jihar suna komawa wasu jihohi.

zamfara killings, kashekashen zamfara

Hakan ya biyo bayan sanarwar da babban sakatarensa a fannin sadarwa ya fitar, Mista Adeniyi Adesina, bayan gwamnan ya yi magana a wurin wani taro, akan gudanar da tsarin tsaro, wanda sarakunan gargajiya, shugabannin hukumomin tsaro, kungiyoyin jama'a, 'yan siyasa, 'yan kasuwa da sauransu suka hallata a Osogbo.


Oyetola ya ce "ya zama wajibi a sanya matakan da za su magance matsalar 'yan ta'adda da ke faruwa a jihar Zamfara shigowa jihar Osun."
Gwamnan ya jaddada bukatar tabbatar da tsaro ta hanyar tattara bayanai, sannan sarakunan gargajiya su saka ido a yankunansu da kuma bukatar a fadakar da jami'an tsaro su sanya ido wurin dakile duk wani shiri na ta'addanci a jihar.

Gwamnan da kuma jami'an tsaro sun gargadi masu bada gidajen haya, akan bai wa mutane wadanda ba su da kyakkyawar masaniya a kansu.

KU KARANTA: A karon farko an yiwa wasu birai dashen kwakwalwar Dan-Adam.
"Idan ka bawa mutumin da baka san shi ba hayar gida, kuma muka gano cewa dan ta'adda ne, to duk abinda ya biyo baya kai ka jawowa kan ka," in ji Oyetola.

Ya bukaci sarakunan gargajiya da su yi aiki tukuru, domin masu hakar ma'adanai suna nan suna yawo a wasu yankuna na cikin jihar.

Gwamnatin tarayya ta hana hakar ma'adanai a jihar Zamfara, bayan ta samu bayanan cewa 'yan ta'addar jihar su na da alaka da masu hakar ma'adanai wadanda ba su da lasisi.

SOURCE LEGIT.NG

Thursday

Jerin mutanen da sojoji suka kashe yayin kai hari akan "yan ta'adda ; Cewar Sarakunan zamfara

A jiya Laraba, 17 ga watan Afrilu, majalisar sarakunan Zamfara sun saki jerin sunayen mutanen garin da harin ya kashe su 11 yayinda aka kaiwa yan bindiga harin a karamar hukumar Zurmi.
zamfara killings

Sunayen sune:

Mai Daji Barau,

Na Dumburum,

Suwaiba Alka,

Yar Guru Na Dumburum,

Maryam Shafiu,

Dahe Malan Sule,

Buhari Dan Kurma,

Zaliha na Dumburum,

Aisha Akilu,

Alamin Alka

Fati ‘Yar Gum.

A cewar sarakunan, wasu mutane 11 sun samu raunuka sakamakon wadannan hare-hare a garin Dumburum, karamar hukumar Zurmi na jihar ranar 9 ga watan Afrilu, 2019.
Sunayen wadanda suka samu raunukan sune:

Haruna Kusu,

Muhammad M Sani,

AbdulRazak Abubakar,

Yakubu Yunusa,

Dan Diyya,

Sa’a Dayyabu,

Yar’wargi Mamman,

Gwamna na Dumburum,

Rashida Alka,

Maryam Akilu

Sadiq Sukuranu.

KARANTA WANNAN : Babu Batun cire tallafin mai a Najeriya - NNPC ta magantu 

Kana sun ambaci cewa akwai mutane 20 da aka harin ya rusawa muhalli.
A hira da manema labarai da suka gabatar a Gusau, Wakilin sarakunan jihar, Sarkin Fulanin Bungudu, Alh Hassan Attahiru ya jaddada cewa hari sojin ya kashe al'ummar gari.

SOURCE LEGTI.NG

Wednesday

"Yan sanda sunyi nasarar damke kasurgumin mai garkuwa da mutane a katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta sanar da kama wani kasurgumin mai garkuwa da mutane a jihar Katsina, jami’in hulda da jama’a na rundunar SP Gambo Isah ne ya sanar da hakan a wata takardar manema labarai da jami’in ya saki yau Laraba a garin Katsina.

Kasurgumin mai garkuwa da mutanen ya yi wa wani dan kasuwa barazanar cewa zai yi garkuwa da shi, in har bai biya Naira miliyan biyu ba, mutumin mai suna Magaji Gudaji mai shekaru 30, wanda ke zama a kauyen ‘Yandoka dake Dayi a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Jami’an ‘yan sandan sun samu nasarar cafke shi ne bayan da suka samu bayanan sirri, inda suka same shi da wayar hannu kirar Itel da kuma layin wayar da yake amfani da shi wajen aikata laifukkan, rundunar ta ga sakon barazanar da ya aike wa da wancan dan kasuwan, kuma tuni ya amsa laifin nashi ma.

Rundunar ta ce da zarar ta kammala binciken ta za ta gurfanar da mutanen a gaban kotun don fuskantar hukuncin da ya dace da shi, sannan tana ci gaba da aikin gano sauran abokan aikata laifin shi Magaji din.

Dalilin Da ya hana mu sakin tubabbun ''yan boko haram 150 : Rundunar soji

Kwamandan sansanin ‘Operation Safe Corridor (OPSC)’ dake garin Mallam Sidi ta jihar Gombe , Kwanel Beyidi Martins, ya bayyana cewa, sun ki sakin tubabbun ‘yan kungiyar ta’addan nan na Boko Haram 150 ne saboda sake farfado da hare haren da aka samu a yankin Arewa maso gabas a ‘yan kwanakin nan. Haka kuma har yanzu ba a kammala cika ka’idojin dake tattare da sakin nasu ba har zuwa yanzu.

An sama da tsarin nan na ‘De-radicalization, Rehabilitation and Re-integration (DRR)’ don samar da yanayin sake shigar da tubabbun ‘yan Boko Haram a cikin al’umma, wannan kuma shiri ne da ya sanu asali bayan da hukumar tsaro na Nijeriya ta yanke shawara a watan Satumba na shekarar 2015. Fiye da ‘yan ta’adda 2,000 suka mika wuya tun da aka fara shirin, inda ko a makon da ta gabata an samu mutum 200 sun mika wuya a jihar Borno.

Kwanel Martins ya ce, ya zuwa yanzu an fuskanci ‘yan ta’adda 260 cikin su a kwai mutum 6 da suka fita dage hannun sojojin. An kuma salami mutum 95 a watan Fabrairu 2018 inda aka mika su ga jihohin su na Adamawa da Bauchi da Borno da kuma jihar Yobe, a halin yanzu suna nan suna ci gaba da harkokin rayuwarsu ba tare da wani matsala ba.

Kashi na karshe na mutum 150 sun kammala samun horonsu a ranar 24 na watan Nuwamba 2018 amma har yanzu suna nan a hannun mu saboda hare haren da ke samu a ‘yan kwanakin nan amman lallai za a sake su a kuma mika su ga jihohin su na haihuwa wanda sun nuna a shirye suke don karbar su tare da shigar da su a cikin harkokin al’umma da zaran an samu saukin hare haren.
An samar da sansanin OPSC tare da hadin gwiwar kungiyoyin kare hakkin bil adam na duniya da kuma dokokin kasa da kasa tare da kuma bin dokoki da tsarin mulkin Nijeriya, an kuma shirya shi ne don karya kadarin mayakan Boko Haram.

Kwamitin lura da harkokin shirin na OPSC ya hada da Shugaban Rundunar Tsaro na Nijeriya, Janar Abayomi Gabriel Olonisakin a matsayin shugaban kwamitin, haka kuma a kwai Gwamnonin Adamawa da Borno da kuma jihar Yobe, haka kuma a kwai shugaban rundunonin sojojin kasa da na sama da shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya da Darakta a ofishin mai bayar a shawara a kan harkokin tsaro ‘National Security Adbiser’ da Darakta Janar na SSS da shugaban hukumar leken asirin kasa da kuma shugaban hukumar bayar da agajijn gaggawa na NEMA a matsayin ‘yan kwamiti.

Kwanel Martins ya yaba wa tsarin shugaban kasa Muhammadu Buhari da Janar Olonisakin da kuma shugabancin da jagoran farko na hukumar Manjo Janar BM Shafa ya bayar don tabbatar da kafuwar hukumar tunda farko.

Ya kuma kara da cewa, ana nan ana sa ido a kan dukkan mutane da aka saki an kuma samar da mutane 375 daga ofishin ‘National Security Adbiser’ da ‘Nigeria Prisons Serbice’ da ‘National Identity Management Commission’ da ‘Armed Forces of Nigeria’ da ‘Nigeria Police Force’ da ‘Department of State Serbices’ da ‘Nigeria Immigration Serbice’ da kuma ‘Nigeria Security and Cibil Defence Corps’ don taimaka wajen sa ido a kan tubabbun.

Sauran bangarorin da aka samar da jami’ai sun hada da ‘Federal Ministry of Women Affairs’ da ‘National Emergency Management Agency’ da ‘National Drug Law Enforcement Agency’ da ‘National Orientation Agency’ da ‘National Directorate of Employment’ da kuma ‘National Youth Serbice Corps’.

Ya kara bayyana cewa, a halin yanzu hankalin ‘yan Nijeriya ya fara karkata a kan harkokin hukumar OPSC bayan da aka samu bayanan dake nuna hannun tubabbun da suka samu horo a hare haren ta’addancin da aka samu a yan kwanakin nan.

A martaninsa ya ce, wadanda suke yin wannnan zargin ba su da cukakken bayanani na yadda hukumar OPSC ke gudanar da ayyukan su. Yana tattaunawarsa da ‘yan jarida a kan hanyarsa ta zuwa cibiyar samar da zaman lafiya na ‘Kofi Anan International Peace-keeping Training Institute’ dake Accra ta kasar Ghana.
Ya nisanta alaka a tsakanin ‘yan Boko Haram da tubabbun ‘yan Boko haram da suka tsira musamman ganin irin halin a yaba da suka nuna a zaman horaswa na makwanni 52 da suka samu a zaman sun a sansanin..

Ya kuma kara da cewa, sun kuma yi rantsuwa a gaban babban mai shari’a na kasancewa maus bin doka da oda, da kuma hanyoyin sa ido da muka sa musu, lallai babu yadda za su koma ga harkokin aiki tare da ‘yan Boko Haram.
Ya kuma kwatanta cibiyar ta OPSC da cewa, ita ce, daya tilo a Nijeriya inda ake yaki da ta’addanci ba tare da makami ba, kuma babu irinta a duk fadin Afrika, harkoin ta kuma ya yi dai dai da yadda ake gudanar da irin ta a fadin duniya.

SOURCE Leadership.ng