Showing posts with label addini. Show all posts
Showing posts with label addini. Show all posts

Thursday

Bidiyo : Wata Sabuwa: Azumin Sitta 6 Shawwal Bidi'a Ne Inji Dr Ahmad Gumi

Dr, Ahmad Gumi Yakaranto A cikin Karatun littafin Imam Malik Cewa Azumin Shida Bayan Ramadan Bidi'a ce.

Asali ma Hadisin Da Ake Kafa Hujja Dashi Ba Ingantacce Bane, cewar ml gumi.



Shahararren Malamin addinin Islama dake garin Kaduna, Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya bayyana cewa azumin guda shida da Musulmai ke yi bayan kammala azumin watan Ramadana, a cikin watan Shawwal bai inganta ba, kuma bidi’a ne.

Gumi ya bayyana haka ne cikin wani bidiyo daya watsa a shafinsa na kafar sadarwar zamani ta Facebook a ranar Laraba, 5 ga watan Yuni, inda yace a fahimtar babban Malamin addinin Musulunci, Imamu Malik, Azumin Sittu Shawwal bai inganta ba, sahabbai, tabi’ai, duk basu yi ba.

Ga Bidiyon Nan Kasa
A cigaba da jawabinsa, Sheikh Gumi ya bayyana cewa, uwar muminai, matar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Aisha, bata rama azumin watan Ramadan sai a watan sha’aban ma, ma’ana da azumin shawwal ya inganta da an ruwaito tayi.

Bugu da kari Gumi ya bayyana ma masu fahimtar sahihancin hadisin dake kira ga azumin sitta shawwal cewa Malik ya san hadisin, kuma Malik a garin Madina ya rayu kafin Annabi ya cika shekaru 150 da mutuwa, don haka ya san hadisin, amma hadisin bai inganta ba. Daga karshe Malamin ya bayyana cewa akwai raini ga Imamu Malik cikin kiran mutane su yi azumin sitta Shawwal, saboda dama a ko ina akwai masu da’a da bin nagaba da kuma masu yin bore ga nagaba. 

Monday

Yanzu Yanzu: An ga wata, gobe take Sallah

Ta tabbata gobe Talata take Sallah yayin da sabon jaririn watan Shawwal ya bayyana a kasar Saudiya.

 An ga wata

Hakika gobe ne 1 ga watan Shawwal na shekarar Alif dubu daya da dari hudu da arba'in bayan hijirar fiyayyen Halitta daga birnin Makkah zuwa Madinah.
A gobe da ta kasance Talata, 4 ga watan Mayun 2019, za a gudanar da shagulgula na bikin karamar Sallah a kasar Saudiya yayin da jaririn watan Shawwal ya bayyana a Yammacin yau bayan an kai azumi na ashirin tara.

Ko shakka ba bu addinin musulunci ya shar'anta yin azumin farilla na tsawon kwanaki ashirin da tara ko kuma talatin a watan Ramadana inda kuma ake gudanar da bikin karamar Sallah watau Eid Ul Fitr yayin da watan jinjirin watan Shawwal ya bayyana.

A yayin da al'ummar Musulmi ke kirdado tare da laluben bayyanar sabon watan Shawwal a Najeriya, a yau ne za a kai azumi na 29 a wannan mafificin wata na Ramadana da aka fara gudanar wa tun a ranar 6 ga watan Mayun 2019.

KARANTA KUMA: Kwana Casa'in - Kashi Na Tara 9 | Cigaban shiri. 

Jaridar Legit.ng ta ruwaito, Sarkin Musulmi Sultan na Sakkwato, Alhaji Abubakar Muhammad Sa'ad, ya hori al'ummar musulmi a Najeriya da su zura idanu tare da fita wajen laluben jaririn Shawwal daga yau daren Talata.


Tuesday

Kungiyar Izala ta gabatar da muhimmiyar bukata a gaban gwamnati

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS) ta bukaci Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi da su karfafa kokarinsu wajen ganin sun samar da isasshen wutar lantarki a fadin kasar.
Bala lau

Kungiyar ta cigaba da yin kira ga gwamnati a dukkan matakai da su mayar da hankali wajen samar da wutan lantarki a yankunan karkaran da ke kasar don inganta samar da ayyuka ga al’umma tare da inganta tattalin arzikin kasar.

Kungiyar ta bayyana kiran ne a taro na kasa na mako 26 na shekara shekara da kungiyan ta gudanar a Jos a ranar Talata, 30 ga watan Afrilu.

Sakon na dauke da sa hannun babban mai gudanarwa na kungiyar na kasa a taro da gasar alkur’ani, Hafiz Aminu Yusuf.

KU KARANTA KUMA: Dalilin Da Yasa Buhari Ya Kulle Ni A Kurkuku – Lamido Adamawa.   
Har ila yau ya bukaci hukumomin tsaro dasu karfafa ayyuka wajen kau da laifuffuka a kasan don guje ma batanci ga martabar kasan.

Kumgiyar ta kuma roki gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da su tabbatar an cimma buri, adalci da gaskiya wajen nadin alkalai a kotun Najeriya.

Friday

Manyan likitoci Biyar sun shigo Nigeria don Duba lafiyar Zakzaky.

A iya cewa wannan shine karon farko da gwamnatin Nijeria ta yarda wasu likitocin kasar waje samun damar ganawa da shugaban yan shi'a, Ml. Ibrahim Zakzaky domin duba lafiyarsa tun bayan kamashi da hukuma tayi a shekarar 2015.
free zakzaky, ml zakzaky

Majiyar ta ruwaito cewa likitocin sun samu damar ganawa da ml. Zakzaky ne bayan samun umarni daga Alkalin wata babbar kotu dake garin Kaduna, wanda ke sauraron karar da gwamnatin jahar Kaduna ta shigar da Al-Zakzaky.

Duba da halin rashin lafiya da shugaban yan shi’an yake aciki ne yasa Alkalin yayi umarni ga hukumar tsaron sirri ta dss wadanda ke rike da Zakzaky da matarsa, dasu gaggauta gayyato masa likitocin da yake so don su duba lafiyarsa data matar sa.

Tunda a farko dai lauyan Al-Zakzaky, Femi Falana ne ya nemi wannan bukata daga Alkalin kotun, bayan ya bata bayanin cewa har yanzu Zakzaky da matarsa suna fama da matsanancin ciwo sakamakon raunuka da suka samu daga harbin bindiga da Sojoji suka yi musu a yayin da suke kokarin kamasu a shekarar ta 2015.

Haka kuwa aka yi, hukumar DSS ta bi umarnin kotu, inda ta baiwa likitocin damar ganawa da Zakzaky da matarsa a ranar Alhamis, 25 ga watan Afrilu a inda suke tsare dasu, sai dai basu bayyana ma manema labaru wata magana game da abin dake damun Malamin ba.

KU KARANTA: Yadda ake mayar da hakora suyi haske ƙal-ƙal a cikin awa daya  

Idan za’a tuna a can kwanakin baya da dadewa an yi ta yada jita jitan Malamin ya mutu a hannun DSS, inda daga bisani hukumar DSS ta karyata batun, har ma ta bayyanshi ga manema labaru, kuma ya bayyana musu cewa yana samun kulawa, amma baya jin dadi sosai.

MAJIYA : LEGIT.NG

Tuesday

Tofa - An kayyade kudin sadakin aure a kafatanin kasar nan

Wani babban Malamin addinin Musulunci a kasarnan, Dr Abdulhameed Shu'aib Agaka, ya bayyana N13,438 a matsayin ainahin kudin sadakin aure a addinin musulunci.

Nawa ne sadakin aure, sadakin aure

Sannan ya kara da cewa, addini ya halatta, idan miji yana da hali ya biya fiye da yanda shari'a ta bayyana.

A lokacin da yake bayani, a gidan radiyo a garin Ilorin dake jihar Kwara, Dr. Agaka, wanda yake tsohon Malami ne a jami'ar Bayero dake Kano, yace duk wani aure da aka yi shi ba tare da an biya sadaki ba, to bai hallata ba a musulunci.

KU KARANTA: (Music Mp3) - Uban Abba Zama Daram - New song by Rarara&Ado gwanja - Download now.

Miji shine yake bada sadaki ga mata, domin nuna girmamawa a gareta, da kuma kara bada tabbacin cewa duk wasu lamura nata sun dawo kanshi.

Sannan ya kara da cewa a musulunce ana iya amfani da shanu, filaye, gonaki, zinare da wasu abubuwa dai masu muhimmanci wurin biyan sadaki.

A karshe Malamin ya shawarci Musulmi da su dinga bin dokar da Allah da Manzonsa suka gindaya, musamman ma ta fannin aure, domin kaucewa zinace-zinace.

Monday

Kotu ta daga sauraron karar El-Zakzaky har sai baba-ta-gani


Wata babbar kotun jihar Kaduna karkashin mai shari'a Gideon Kurada ta daga sauraron karar da gwamnatin jihar Kaduna ta shigar da shugaban kungiyar mabiya shi'a (IMN), Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, har sai baba-ta-gani.

shari ar zakzaky


Alkalin kotun ya bayyana cewar ya daga sauraron karar ne ba tare da saka ranar dawowa ba saboda nadin da aka yi ma sa a matsayin alkali a kotun sauraron korafe-korafen zaben shugaban kasa da na mambobin majalisar tarayya. Tun a shekarar 2015 gwamnati ta kama El-Zakzaky tare da matar sa, Zeenat, biyo bayan wata kazamar arangama tsakanin mabiyansa da dakarun sojin Najeria a garin Zaria dake jihar Kaduna.

Rahotann sun bayyana cewar an kashe mabiya shi'a kimanin su 300 yayin artabu da dakarun sojin. Ana tuhumar El-Zakzaky da matar sa da hada baki domin aikata kisa, taro ba bisa ka'ida ba, da tayar da tsugune tsaye da sauran su.

DUBA WANNAN :- Kano: Jami'an tsaro sun bawa hammata iska a cibiyar tattara sakamakon zaben gwamna. 

Da yake gana wa da manema labarai bayan yanke hukuncin kotun, Femi Falana, lauyan dake kare wadanda ake tuhuma, ya ce wadanda yake karewa basu samu damar bayyana a gaban kotu ba saboda yanayin rashin koshin lafiya da su ke ciki. Ya ce tun ranar 14 g watan Disamba na shekarar 2015 da aka rufe su, ba a bawa lafiyar su kulawa ba, tare da bayyana cewar su na matukar bukatar a duba lafiyar su. Read more:

Kalli zakakuran da zasu wakilci Najeriya a gasar Al-Qur’ani ta duniya

An sanar da jerin sunayen zakakuran daliban Najeriya kuma mahaddata Al-Qur’ani da zasu wakilci Najeriya a gasar haddar Qur’ani ta duniya gaba daya da zata gudana a kasar Turkiyya, a watan Mayun shekarar 2019.
Mahaddata Alqurani, na kano

Majiyar Legit.ng ta ruwaito daga cikin wadanda zasu wakilci Najeriya a fannin Maza akwai Alaramma Abdurrahman Bunu daga jahar Bornu, da kuma Yusuf Yahaya daga jahar Edo, dukkaninsu sun ciri tuta wajen rera karatun Qur’ani da tajwidi.

KU KARANTA: Dalilin da ya sa ba mu yi abin da Buhari yace a Kano ba – inji Kwankwaso

Kungiyar cigaban Musulunci ta Najeriya, IPIN tare da hadin gwiwar gidauniyar Diyanet ta kasar Turkiyya ce suka shirya gasar sharan fagge a Najeriya, wanda ya gudana a babban Masallaci dake babban birnin tarayya Abuja, daga nan aka zabi wadanda zasu wakilci Najeriya.

Sakamakon gasar da aka kammala a Abuja ya nuna Alaramma Bunu ne yazo na daya a haddar izu sittin, yayin da Ismail Umar daga jahar Neja, da Abdulmalik Ahmad daga jahar Ogun suke bi masa.

Haka kuma Malam Yahaya yazo na daya a haddar Tangeemi, yayin da Ibrahim daga jahar Borno, da Ajmul Nura Shema daga jahar Katsina suka rufa masa baya a matsayin na biyu da na uku.

A bangaren Mata kuwa, Maimuna Abdurrahman daga Abaji ce ta zama zakakura a haddar izu 5, yayin da Aisha Sani daga Kuje ta lashe gasan haddar izu 10, Fauziyya Shehu daga AMC ta lashe haddar izu 20, Halima Muhammad Gwagwalada ta lashe izu 40, sai Surayya Muhammad ta lashe izu 60.

Dayake nasa jawabin, shugaban IPIN, Dakta Muhammad Kabir Adam ya bayyana cewa sun fara shirya gasar ne a shekaru hudu da suka gabata don karfafa ma daliban ilimi haddan Al-Qur’ani da sauti mai dadi da kuma tajwidi.

Saturday

Wata kotu a kasar Iran ta yankewa wata yar fafutukar kare hakkin bil adama hukucin bulalai 148 da zaman gidan kurkuku na tsawon shekaru 38 sakamakon yadda take yaki da sanya Hijabi a kasar ta hanyar da'awar wayewar kai.

Mijin matar mai suna Reza Khandan, wanda ya garzaya shafin ra'ayi da sada zumuntar Facebook domin bayyanawa duniya halinda uwargidarsa ke ciki. Ya wallafa cewa matarsa mai suna Nasrin Sotudeh, na tsare hannun hukuma bisa ga zargin kyamar hijabi.

A yanzu haka, kotu ta yanke mata hukuncin shan bulalai 148 sannan zaman gidan wakafi na tsawon shekaru 38.

KU KARANTA: Yan asalin jihar Kano mazauna Amurka da Turai sunce suna tare da Ganduje

A cewarsa bai san iya adadin shekarun da za ta yi a kurkuku. Saboda hirarsa da Nasrin na dan kankanin lokaci ne. Basu samu damar yin dogayen bayanai ba. Amma tana garkame a yanzu haka a gidan wakafin Evin,ta sanar musa cewa, hukuncin farko, shekaru 5 ne,inda na biyu kuma, shekaru 33 da bulalai 148.

Ana zargin Nasrin Sotudeh da aikata wasu manyan laifuka 7,wadanda suka hada leka sirrukan gwamnatin Iran,yawo ba tare da hijabi ba da kuma da'awar hana matan kasar rufe kawunansu." inji lauyan wacce ake tuhuma.
A shekarar 2012, Tarayyar Turai ta karrama Sotudeh da lambar yabo ta Sakharov sabili da 'yancin bayyana ra'ayoyinta.

Tuesday

Asalin tsafi : kissar Haruta Da Maruta.

QISSAR HARUTA DA MARUTA

.

Asalin tsafi.

.
Shin Mala'iku Ne Su Ka Koyar da Tsafi?

Kissar Haruta da Maruta, Haruta da Maruta, Tsafi, Aslin tsafi, Tauraruwa zara


Daga Cibiyar Tarbiyyah Islamiyyah, Masu Yin Ruq'yah Da Harhada Magungunan Musulunci. Lambar waya 08162600700.

Allah Madaukakin Sarki Ya ambaci sunayen Haruta da Maruta sau daya a cikin Alqur'ani mai girma, acikin Suratul Baqarah.

Ruwayoyi da dama sun zo akan Qissar wadannan sunaye na Mala'iku ko kuma Sarakuna amma dai za mu dauki jigon ruwayar da Ahmad ya fitar acikin Musnad, da kuma ibnu Hibban aciki Sahihinsa daga ibn Umar رضي الله عنهما
sai mu shigar da bayanin sauran ruwayoyin a ciki.
..

Ga cikakkiyar Qissar :

.Lokacin da Allah Madaukakin Sarki Ya saukar da Annabi Adam ﻋﻠﻴﻪ السلام
daga Aljanna zuwa kasan duniya, sai Mala'iku suka dinga cewa "Ya Ubangiji, yanzu ka sanya wadanda za suy 6arna su dinga zubar da jinin junansu a duniya?!, alhali mu muna girmamaKa tare da gode maKa kuma muna kaskantar da kai a gareKa?".

Sai Allah Ya ce "Ni Na san abinda baku sani ba".

Sai su ka ce "Ya Ubangiji mu fa mun fi yi maKa biyayya sama da 'yanAdam, inda mu ne ka saukar da  mu duniya to ba za mu sa6a maka ba".
Sai Allah Ya ce musu "To ku kawo Mala'iku guda biyu a cikinku. Sai Mu saukar da su kasan duniya, don Mu ga yadda za su yi. (za suyi biyayya ko ba za suy ba?!)".
Sai suka ce "Ya Ubangiji Ga Haruta da Maruta mun za6e su a kaisu"

.
Sai aka saukar da wadannan Mala'iku biyu zuwa duniya, aka sauke su a garin Babila.

Lokacin da aka sauke su sai aka ce musu ga Tsafi nan ku dinga koyawa mutane amma duk wanda ya zo zai koya ku gaya masa in ya aikata ya zama kafuri.

A wata ruwayar kuma an ba su Sihiri ne domin su dinga yiwa mutane gargadi akan su guje shi kada su aikata shi.

To bayan an saukar da su sai Allah Ya mayar da Zahr', wato wannan babbar tauraruwar da muke gani a kuma da wata, sai aka mayar da ita siffar mace.

Sai ta zo wajensu a sura kyakkyawa.

 Da su ka ganta sai su ka nemeta. Sai ta qi amincewa ta ce musu "Saidai in za ku kafurta to zan yarda da ku".
Da su ka ji haka sai su ka ce basu yarda ba.

Sai ta fi, ta sake dawowa da wani jariri a hannunta. Sai su ka kuma nemarta. Sai ta qi amincewa,  ta ce "Saidai in za ku kashe wanan yaron, to zan ba ku hadin kai".

Sai su ka ce basu yarda ba. Sai ta tafi, ta sake dawowa da tukunyar giya a hannunta.

Suka nemeta. Sai ta ce bata yarda ba sedai in za su sha giya tukuna. Sai su ka yarda su ka sha giyar.

Bayan sun sha sai maye ya kama su, su kayi zina da wannan matar sannan kuma suka kashe wannan jaririn.

Lokacin da suka farka sai Allah Ya tambayesu alqawarin da sukayi akan ba za su sa6a masa ba.

Daga nan sai aka ba su za6i akan su za6i irin azabar da  za ayi musu. Shin a duniya suke so ayi musu azaba ko kuma a bari sai an je Lahira?!.
.
Sai suka ce ai azabar Lahira bata karewa, mun za6i ta duniya.

Shikenan sai aka kai daya inda rana take 6ullowa. Kullum idan rana ta 6ullo sai ta tafasa masa kansa.

Dayan kuma sai aka kaishi inda rana take faduwa, kullum in rana zata fadi sai ta kona shi.

Ita kuma Zahra' sai aka mayar da ita tauraruwa ta koma sama.
.
To a lokacin ne aka ba su sihiri, (bisa sa6anin ruwaya).

Sai aka ce duk wanda ya zo yana so su koya masa.

Sai suka dinga koyawa mutane da Aljanu yadda ake raba tsakanin miji da mata amma basa koyawa kowa sai sun ce masa "Tabbas mu fitina ne!, don haka kada ka kafurta".

In Mutum ko Aljan ya yarda zai kafurta sai su koya masa.

Daga nan sai harkar Sihiri da tsafi ta yadu a tsakanin mutane da Aljanu.
.
Malamai sun yi raddi sosai akan wannan qissa musamman kasancewar Mala'iku basa sa6o da kuma maganar cewa su ne suka koyar da tsafi sannan ruwayoyin yawanci Isra'iyliyyat ne, sedai abinda aka samu na 6angarorin qissar daga Alqur'ani da kuma ruwayar ibnu Umar daga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم
kamar yadda muka ambata.
.
Harkar Bokanci, Sihiri, Tsafi, Surkulle, Rufa-ido, Tsibbace-tsibbace da makamantansu, sun samu shahara sosai da kar6uwa a wajejen aiko Annabi Sulaiman عليه السلام
shi yasa ya zamto yana daga cikin manyan abubuwan da Annabi Sulaiman yay fada  da su kuma ya yaqi masu aikata shi.

Sannan wannan harka ta samu kar6uwa ne da matsayi da shiga zukatan al'umma a wajenjen zamanin Annabi Musa عليه السلام،
inda a lokacin ake ganin wanda ya iya sihiri tamkar wani shugaba kuma wani abin ay wa biyayya sannan abin tsoro.

Za mu kawo cikakkiyar qissar yadda Annabi Sulaiman عليه السلام ya yaqi masihirtan zamaninsa da kuma dalilin da yasa bayan ya  yi wafati Shaidanu suka ce ya mulki duniya ne ta hanyar tsafi.
.
Sannan za mu sake duba qissar Haruta da Maruta tare da bayanin yadda Annabi Musa ya fuskanci matsafan zamaninsa.
.
Duk wannan zai zo insha Allahu a cikin posting din mu mai taken "ASALIN TSAFI", Domin Allah Madaukakin Sarki Ya fada acikin Suratuz Zariyari cewa:
.
ﻓَﻔِﺮُّﻭﺍ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺇِﻧِّﻲ ﻟَﻜُﻢْ ﻣِﻨْﻪُ ﻧَﺬِﻳﺮٌ ﻣُﺒِﻴﻦٌ * ﻭَﻻ ﺗَﺠْﻌَﻠُﻮﺍ ﻣَﻊَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺇِﻟَﻬﺎً ﺁﺧَﺮَ ﺇِﻧِّﻲ ﻟَﻜُﻢْ ﻣِﻨْﻪُ ﻧَﺬِﻳﺮٌ ﻣُﺒِﻴﻦٌ * ﻛَﺬَﻟِﻚَ ﻣَﺎ ﺃَﺗَﻰ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻣِﻦْ ﻗَﺒْﻠِﻬِﻢْ ﻣِﻦْ ﺭَﺳُﻮﻝٍ ﺇِﻻَّ ﻗَﺎﻟُﻮﺍ ﺳَﺎﺣِﺮٌ ﺃَﻭْ ﻣَﺠْﻨُﻮﻥٌ ‏[ ﺍﻟﺬﺭﻳﺎﺕ :50 - 52] .
.
Ma'ana:
 "Kamar haka ne (Su wadannan mutanen) babu wani Annabi da ya zo wajen wadanda suka gabace su face sai sun ce masa mai Sihiri ko kuma mai hauka".
.
Wannan ayah tana nuna cewa tun zamanin Annabi Nuhu  ﻋﻠيﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ
duk da cewa shi ne farkon Manzanni, duk Annabin da Allah Ya aiko sai Kafurai sun ce masa mai sihiri ne. Kenan tun a lokacin ana yin sihiri.

Wasu Malaman kuma suna ganin sihiri ya samo asali ne daga hannun Aljanu kuma dalilansu sun fi karfi gaskiya.

Insha Allahu za mu cigaba da kawo muku bayanai masuamfani, zasu zo nan gaba kadan da yaddar Allah.

Monday

[Audio] Martani Ga Rabiu Musa Kwankwaso :- Download now

MARTANI ZUWAGA RABIU MUSA KWANKWASO AKAN MAGANAR DA YAYI GA MALAMAI MAGADA ANNABAWA.


Rabiu kwankwaso

Wani bawan Allah mai suna Abdullahi musa gwale ya mayarwa da kwankwaso martani akan maganganun da shi kwankwason yakeyi akan maluman addinin musulunci, idan baku manta ba a ranar asabar da ta wuce ne kwankwason yasake furta wani batu akan malam,

Abdullahi Musa ya bayyana cewa su daliban Addini baza su yarda da irin wannan maganganun cin mutunci da kwankwaso yake furtawa ba, inda ya kira kwankwaso kangaarren dan siyasa, kamar yadda zakuji acikin wannan Audio.Sannan yace kamar yadda kwankwaso yace yana ganin malaman tsirara to suma haka suke kallon sa.

 Ya fadawa kwankwaso cewa malaman Addini suna da tacewa akan siyasar.zakuji sauran martanin nashi acikin wannan audio.

PLAY NOW


OR


DOWNLOAD NOW


Sunday

YADDA AKE YIN ISTIKHARA : Neman zabin Allah.

YADDA AKE YIN ISTIKHARA : Neman zabin Allah.



* Neman zabin Allah, wata sallah ce mai raka'o'ibiyu, wacce yinta sunnah ce mu'akkada (sunnahce mai karfi), wacce manzon Allah ya koyar dasahabbansa ita har tazo garemu kamar yadda al-qur'ani ya iso gare mu, sallace da akeyi yayinneman zabin Allah akan wani al-amari kamar;aure, sayan gida/mota aikin gwabnati da daisauransu, sai dai ita wannan sallar ba'ayintaakan abunda yake wajibi ko mustahabbi akan ka;kamar neman zabin Allah akanyin azuminramadan, ko salloli biyar na yini, ko fitarda zakka,azumin alhamis da litimin da dai sauransu.

* Sai dai wurin Mustahabbi ana iyayi idan suncikaro, misali: mutum ne yake son yaje umra karona biyu a lokaci guda kuma yana so yaje watakasa neman ilimi, to yana iya neman zabin Allahakan ya zaba masa wanda yafi Alkhairi a cikin su.

* Hakika Duk wanda ya nemi zabin Mahalicci,kuma ya yi shawara da talikai muminai, kuma yayi azama a cikinlamarin sa, to ba zai yi nadama ba Insha Allah.Domin Allah Madaukakin Sarki ya ce: "Kuma kashawarce su cikin lamarin ka, idan kuma kaquduri aniya, to ka dogara ga Allah" [Ali-Imran :159].

* Hadisi ya gangaro Jabir ibn Abdullah, Allah yakara yarda dashi da Maihaifin saya ce : Manzon Allah (SAW) ya kasance yanakoya mana yin Istikhara (neman zabin Allah) acikin dukkanin al'amura kamar yadda yake koyamana sura daga cikin surorin Alqur'ani. Ya kance: ''Idan dayanku yayi niyyar yin wani al'amarito yayi sallah raka'a biyu ba farillah ba sannanya ce:
"Allaahumma innii astakhiiruka bi ilmika,wa'astaqdiruka bi kudiratika, wa'as'aluka minfadlikal azeem, fa innaka takadiru wala akadiru,wa ta'alamu wala a'alamu, wa anta allamulguyube, Allahumma inkunta ta'alamu anna hazalamri kharal lii fii deenii wama'ashii wa'akibati amrii, aajilihi wa'aajilihi faqadirhu lii wayassirhulii thumma baariklii fiihi, wa'inkunta ta'alamuanna hazar amra sharrullii fii deenii wama'ashiiwa'akibati amrii aajilihi wa aajilihi fasrifhu'anniiwasrifnii anhu wakadur liyal khaira haithu kaana thumma raddini bihi."
Da Harshen Larabci

MA'ANA

"Ya Ubangijina! ina neman zabin ka da ilimin Ka,kuma ina neman tabbatuwar ikon Ka, ina rokanfalalar Ka Mai gaima, Kai ke da iko ni banda shi,Kai ne Masani ni ban san (komai ba) Kai nemasanin abin da yake boye. Ya Ubangiji na! Inkana ganin wannan abu ('sai ya fadi abin da yakeistiharan a kai') shi yafi min a addinina da rayuwata da qarshen lamarina, to ka tabbatar min dashi, ka sauqaqe min sannan ka yi min albarka acikinsa, in kuwa kana ganin wannan abu sharri negare ni a addinina da rayuwata da qarshenlamarina, ka juyar da shi daga gare ni, ni ma kajuyar da ni dagagare shi, ka kudurtarmin da alkhairi sannan kaamintar min da shi" [Bukhari]

* Na tabbata banbanci ya bayyana a fili gama'abota hankulla da tunani tsakanin wannankarantarwar ta shugaban talikai SAW, da Tsirfe-tsirfe da shafi fadin, wasu marubuta littattafankarya don neman kudi, da masu tsibbace tsibbace

* Ita dai wannan Sallah Mustahhabbi ce anso kayita (domin sunnah ce mai karfi, sannan zakasamu lada idan kayi), amma idan bakayi babalaifi.

* Wannan Addu'a ta istarawa ana yin tane bayanka sallame, sallar nan da kayi mai raka'a biyu,duk da wasu malaman na ganin ana karanta tane,bayan tahiya da salatin manzon Allah SAW kafinSallama, domin mafi Al-khairin bijiro da addu'aacikin sallah shine sujuda da bayan tahiya, saidai magana mafi rinjaye shine bayan Sallama.Allah shine Mafi Sani..* Babu Laifi ga mutum ya maimaita istakharasama da daya, hakam ya tabbata daga cikinmagabata, kamar Abdullahi dan zubair Allah yakara yarda dashi yayi istakhara sau ukku.[Muslum - 970].

* Babu wani hadisi daya inganta da yazo dasurorin da ake karantawa, a cikin sallar nemanzabin Allah.

* Haka kuma babu wani hadisi da yazo dagaAnnabi cewa idan mutum yayi istakhara zaiyimafarki ko zaiga wani mutum yana yi masabayani al-amarinsa.

* Babu shakka duk wanda yayi zai samu natsawucikin abunda Allah madaukakin sarki ya zabamasa.

* Ba mafarki ake yi ba kamar yadda mutanedayawa suka dauka, ana ganewa ne da yanayinnutsuwar zuciya, idan aure ne sai kajizuciyar kata qara nutsuwa da yarinyar, idan sana'a ne kakeso ka farasai kaji zuciyar ka tanutsu da sana'ar.

* Za'a iya yin wannan sallah raka'a biyu da rana,ba dole sai da daddare ba, sannan zaka yita nedaga lokaci zuwalokaci har sai ka sami biyan buqata, sannan Anayin tane koda lokacinda aka hana yin sallah ne,idan bukatar hakan ta taso, domin ita tana dagacikin "Nawafilul Asbab" - "Nafiloli masu dalili".

* Wannan kenan don gane da abunda ya shafiSallar neman zabin Allah madau kakin Sarki,Muna fatan Allah ya bamu damar Ayki Abundamuke rubutawa da karantawa Ameen.

ALLAH YA TAIMAKE MU Ameen

Monday

ALLAH YAYIWA MAWALLAFIN LITTAFIN HISNIL'MUSLIM RASUWA

INNA LILLAHI WAINNA ILAIHI RAJIUN.

JAMA'AR MUSULMI MUNYI BANBAN RASHI.

Allah yayiwa Ash'sheik Sa'id bin Ali bin wahaf Alqhtani Rasuwa A yau litinin, Ash' sheik sa'id Shine wanda ya rubuta wannan shahararren littafi da duk wani musulmi ya sani. Wato HUSNIL'MUSLIM , Littafin da yake dauke da ingantattun addu'oi.



Za'a yiwa Gawar Ash'sheik Sa'id sallah yau litinin a masallacin arrajihy dake garin riyadh Babban birnin kasar saudiyya bayan sallar la'asar, .

Ash' Sheik Allah ya Kyauta makwanci , ya baka ladan wannan hidima ta rubuta wannan shahararren littafi a duniyar musulunci.

®Share®

Tuesday

Gwamnatin tarayya ta ba da hutun kwanaki 2 don bikin Sallah

Ministan cikin gida, Abdulrahman Danbazau ya sanar da ranaku biyu a matsayin ranakun hutun Sallah babba.

- Danbazau ya bukaci yan Najeriya da suyi
amfani da ranakun biyu, 1 ga watan Satumba da
4 ga wata don yiwa kasa addu’an samun zaman lafiya
- Ya kuma gargadi yan kasa masu kalaman
batanci da su guje ma haka domin gwamnati
bazat lamunta ba.

Gwamantin Tarayya ta amince da ranakun
Juma’a, 1 ga watan Satumba da kuma Litinin, 4 ga watan Satumba, a matsayin ranakun hutun Sallah Babba.

Ministan cikin gida, Abdulrahman Dambazau
ne sanar da haka, a madadin gwamnatin
tarayya, inda ya ke taya daukacin al’umman musulmai da ‘yan Najeriya baki daya murna.

Ya kuma yi addu’ar gudanar da shagulgulan
sallah lafiya, tare da samun zaman lafiya da hadin kan kasar nan.
Danbazau ya bukaci yan Najeriya da suyi
amfani da ranakun biyu, 1 ga watan Satumba da 4 ga wata don yiwa kasa addu’ar samun zaman lafiya.

Gwamnatin tarayya ta ba da hutun kwanaki 2 don bikin Sallah.

Ya kuma tabbatar dasamun zaman lafiya tare da kare rayuka da dukiyoyin jama’a, ya na mai umartar jami’an tsaro su tabbatar da wanzuwar hakan.

Ministan ya yi tir da munanan kalaman
kiyayya ya na mai gargadin masu zuguguta
kalaman su kuka da kan su.

More Picture's : A karon farko an daura auren wasu kattin maza su biyu masu ikirarin su Musulmi ne a kasar Ingila.






A karon farko an daura auren wasu kattin maza su biyu masu ikirarin su Musulmi ne a kasar Ingila.

Jahed Choudhury dan shekara 24 ya angwance da abokin Luwadinsa Sean Rogan mai shekara 19 a sigar auren Musulunci a kotun daura aure dake Walsall

Hausa times ta ruwaito yan luwadin Biyu sun kasance tare tsawon shekaru Biyu, Bayanai sunce soyayya ta kullu ne tsakanin yan Luwadin a lokacinda Sean ya yi kicibis da matashi Choudhury na kuka cike da damuwa zaune a akan wani Benci a garin Darlaston.

Bayan mista Sean ya lallashi matashin ya bashi gagarumin taimako daga nan sai ya cigaba da yaudararsa ta hanyar bashi kulawa da kaytuttuka har ya koya masa Luwadi.

Duk da cewa iyaye da yan'uwan Choudhury sun kauracewa wannan fasikanci tare da Allah wadai kuma suka ki halartar auren amma hakan bai damu matashin ba domin a cewarsa "Sean yayi masa gata a lokacinda yake cikin matsananciyar damuwa"

Suna masu bayyana cewa sunyi farinciki da auren junansu da sukayi musamman ganin cewa su Musulmu ne domin yin hakan zai nunawa duniya cewa musulunci bai hanasu cika burinsu ba.



Wednesday

Salah mistakes series : A free Guide video

Salah mistakes series : A free guide video WATCH VIDEO ONLINE
Ya kai Dan uwa, Ya ke "Yar uwa, ku daure ku kalli wannan videon domin gyara tsakaninka da mahaliccin ka , Saboda ita sallah itace ta farko a cikin gerin rukunan musuluncin nan guda biyar, ganin haka ne ma yasa mukace bari mu bayar da wannan videon don gani da kuma kwaikwayon yadda Annabi Muhammad S.A.W ya dinga gudanar da sallarsa a iya tsawon rayuwarsa da fatan Allah ya karbi sallolin da muke gabatarwa Ameen
CLICK HERE TO DOWNLOAD VIDEO

Thursday

GUDUNMAWAR SHEIK ZAKIR NAIK GA MUSULUNCI DA KUMA KALUBALEN DA YAKE FUSKANTA.


  • TARIHIN RAYUWARSA A 
  • TAKAICECikakken sunansa shine Zakir Abdulkareem Naik.

An haife shi a ranar 18 Oct. 1965 a birnin India na Mumbai a Maharashtra.
Zakir ya hallaci makarantu da dama inda ya samu shaidar zama likitan tiyata wato
"Bachelorof Medicine and Surgery".


   zakir naik,zikr,naik,zikr naikSheik Dr. Zakir Naik


Zakir Naik na tare da mai dakinsa Farhat
Naik, dakuma 'yaya biyu Fariq Naik da Rushdaa Naik. .

Zakir Naik ya tsinci kansa cikin sahun masuDa'awah a shekarar 1991, lokacin da Muslunci ya tsinci kansa cikin tsangwama da muwiyacin hali a kasar India saboda gallazawar da masu addinin Hindu kewa Muslunci da Musulmi.

Zakir ya tasirantu ne da salon da'awar
sannanen malam nan wato Sheikh Ahmad Deedat wanda
Zakir ya hadu dashi a shekarar 1987, kamar yadda Naik na sheda a 2006, saboda tarin baiwa ta ilimi da Allah yayiwa Zakir yasa Deedat da kansa yake masa lakabi da "Deedat-Plus" wato kamar kace, "Malam da rabin Malam".

  • RUGUZA MASALLACIN BABRI
A shekarar 1992 wani muhimmin al'amari ya faru. A ranar 6, ga watan Disamba, na shekarar 1992, masu bin addinin Hindu kimanin 150,000 da taimakon jam'iyun siyasa na India; Bharatya Janata Party (BJP) da Vishva Hindu Parishad (VHP) suka afkawa gami da rugurguza Masjid
(masallacin) Babri mai dadden tarihi a cikin garin Ayodhya bayan haka suka ruguje masallatai masu yawa a yankin, masallacin Babri an gina shine tun qarni na 16 kimanin shekaru 500 da suka
wuce. Rushe masallacin ya jawo gagarumar riga wadda tayi sanadiyar asarar dukiyoyi masu tarin yawa da kuma mutuwar mutane fiye 2,000 wadanda yawancinsu Musulmi ne.

Hakika wannan rigima ta kara jefa Musulman India cikin halin ha'ula'i, zullumi da kaskanci, suka zamo basu da wata ta cewa, Muslunci ya zama abin zolaya gami da tsokana. Ana cikin wannan hali ne, Allah yayi nufin dawo
da martabar Muslunci da Musulmi ta hannun Sheikh Dr. Zakir Naik, kamar yadda Muhammad Reyaz ya sheda.


  • DEBATES DINSA
Dr. Zakir ya fara mahawararsa (debate) ta farko a 1994 kan wani littafi mai suna "Lajja" wanda wata mashahuriyar mai aibata muslunci Taslima Nasreen 'yar kasar Bangladesh ta wallafa. Haka a shekarar 2000, Zakir yayi mahawara
da sanannen masanin kimiyar nan Dr. William Campbell a birnin Chicago ta Amurika.

Campbell ya kwashe shekaru yana nazari kafin daga bisani ya wallafa wani littafi da yace Qur'an yaci karo da kimiyar zamani (modern science).
Muhawarar mai taken "The Qur'an and the Bible in the Light of Science" ta daukaka Naik saboda yadda yayi kaca-kaca da littafin da aka dau shekaru ana wallafa shi da hujja cikin kankanin lokaci,
hakan yasa Zakir ya zama abin tsoro tsakanin masu yiwa Muslunci zambo, kamar su Ali Sina wani dan asalin Iran mai tsananin adawa da Muslunci.
.
Zakir Naik wanda zaka iya kwatanta
kwakwalwarsa data "computer" saboda
kaifin rike abu, ya gudanar da lakcoci kusan 4000 a fadin duniya baki daya wanda ya hada da zuwansa Nigeria har sau biyu.


  • NASARORINSA
A bisa kokari irin nasa Zakir ya samar da:

i :- tashoshin satellite na Peace TV English, Peace TV Bangla, Peace TV Urdu da kuma Peace TV Chinese. Tashoshin wadanda babu kamar su wajen yada addini, kimanin mutane miliyan 150
ne suke iya kama Peace TV a kasashe fiye da 200.
Zakir Naik ya samar gami da jagorantar

ii :- "Islamic Research Foundation" (IRF) wato cibiyar bincike ta addinin Muslunci, a karkashin IRF aka samar da (IIS) wato "Islamic International School".

iii :- Sai kuma (UIA) "United Islamic Aid" wadda aikinta shine bada tallafin karatu ga nakasassuda masu rauni.

Irin wannan nasarori da Zakir Naik ya samu, gami da dawo da martabar Musulmai a India dama duniya baki daya, sune suka tsone idanun
munafukai musamman masu son gani bayan Muslunci, tako wace fuska.

Gazawar masu son ganin bayan Muslunci a sakamakon Zakir, yasa suke kokarin ganin bayansa, ta hanyar tsomashi cikin ayyukan ta'addanci, zargin da ako yaushe yake musawa.
Karku manta jam'iyar Bharatya Janata Party (BJP) wacce ta taka rawa wajen gallazawa Musulman India itace ke mulki yanzu. Kuma Prime Minister na yanzu Narendra Modi babban
yaron Lal Krishna Advani ne, wanda ya
jagoranci ruguza masallatan Ayodhya a 1992. Saboda haka babu mamaki cikin sabon salon rufe bakin Musulmai ta hanyar gamawa da Zakir Naik a farko.
.
  • MUSULMAI MASU ADAWA DASHI.
Yawancin masu adawa Zakir Musulmai 'yan Shi'a ne, suna zarginsa da rashin yin biyayya ga dokokin zamantakewa na India daga cikinsu akwai: Kalbe Jawad Naqvi da kuma Yasoob Abbas dss.

Amma yawancin qungiyoyin musulmai na mara masa baya kamar su: Sheikh Abdulkadir Jilani Foundation, Darul Uloom da kuma All-India Sunni Board.


  • BARAZANA GA RAYUWARSA
. A ranar 13 ga watan Juli 2016 shugabar
Vishva Hindu Parishad (VHP) wato Sadhvi ya bada sanarwar bada tukyici na dalar Amurika $78,000 ga duk wanda ya fillo kan Zakir Naik. Hakan yazo kwana daya bayan wata kungiyar Shi'a maiwa
kanta laqbi da Hussaini Tigers. ta sanya ladan $23,000 ga wanda ya kashe Zakir Naik.


  • DAUKAKARSA
Zakir ya sami zama mutum na 89 cikin
mutane 100 dake da karfin fada aji a India kasar dake da mutane fiye da biliyan daya da miliyan dari uku.
(1.3 bn) ya sake zama na 82 a shekarar 2010 kamar yadda The Indian Express ta sanar.

Sunday

Sheik Zakzaky Ya Raba Kayan Abinci Ga Mabukata A Zariya.

An fara rabon tallafin ne tun daga ranar
Talatar da ta gabata.



Kamar yadda ya saba a duk shekara a lokaci
irin wannan watan Ramadana, jagoran
harkar musulunci a Najeriya, Shaikh
Ibraheem Zakzaky na raba kayan abinci ga
mabukata a duk lokacin da watan Ramadana
ya gabato. Kayan abincin wanda suka hada
da shinkafa, masara, gero, suga ,taliya da dai
sauran su.


A bana ma kamar kowacce shekara, duk da
Shehin Malamin na daure a hannun
gwamnatin tarayya, amma ya yi umurni da
'yan uwansa na jini da wasu ba'adin
almajiransa da a baiwa duk wadanda aka san
yana baiwa wannan tallafi a lokacin da yake
nan a duk Unguwannin Zariya. Kuma tallafin
na bana na kayan abincin ya nunka na
koyaushe yawa. Kuma tuni aka mika su ga
inda ya dace.

Kamar yadda NAIJ.com ke da labari, dan
uwansa Sayyid Badamasi Yaqoub ne ya
jagoranci raba kayan tallafin. An fara rabon
tallafin ne tun daga ranar Talatar, 23 ga
watan Mayu da ta gabata.
Kayan abincin da Shaikh Ibraheem Zakzaky ya ce a
rabawa talakawa a Zaria



Al'ummar da suka amfana da wannan tallafi
sun yi matukar godiya bisa wannan
karamcin da Shehin Malamin yake nuna
musu duk da kuwa yana daure, har da
mamakinsu na ganin yadda bai manta da su
ba. Tare da yi masa addu'ar fatan alheri.
Lokacin da ake raba kayan abincin

A makon da ta gabata ne dai gwamnatin
tarayya ta ce bata da niyayr musgunawa El-
Zakzaky da ake cigaba da tsarewa a birnin
Abuja. Sai dai kuma tana bashi kariya daga
barazanar da ke iya tashi sakamakon samun
'yancinsa.

Monday

WELLCOME TO RAMADAN

WELLCOME TO RAMADAN

Allaah has made fasting Ramadaan and spending its nights in prayer out of faith and in the hope of reward a means of forgiveness of sins, as was proven in al-Saheehayn (al-Bukhaari, 2014; Muslim, 760)

From the hadeeth of Abu Hurayrah according to which the *Prophet (peace and blessings of Allaah be upon him) said: “Whoever fasts Ramadaan out of faith and in the hope of reward, his previous sins will be forgiven.” And al-Bukhaari (2008) and Muslim (174)

also narrated from Abu Hurayrah that the Prophet (peace and blessings of Allaah be upon him) said: “Whoever spends the nights of Ramadaan in prayer out of faith and in the hope of reward, his previous sins will be forgiven.”*

The Muslims are unanimously agreed that it is Sunnah to pray qiyaam at night in Ramadaan. Al-Nawawi said that what is meant by praying qiyaam in Ramadaan is to pray Taraweeh, i.e., one achieves what is meant by qiyaam by praying Taraaweeh.

☝ *DON'T FORGET TO SHARE.*  

More stickers 

        

Thursday

Jawabin Jagoran Juyin Islama A Birnin Mashhad : iran








Jagoran juyin Islama na kasar Iran Ayatollah
sayyid Ali Khameni ya gabatar da jawabia gaban
dubban mutanen da suka taru a cikin hubbaren
Imam Ridha (AS) da ke birnin Mashhad, kamar
yadda ya saba yi a farkon kowace shekara ta
hijira shamsiyya.

Kamfanin dillancin labaran IRIB ya bayar da
rahoton cewa, a yayin jawabin nasa, jagora ya
jaddada muhimamncin mayar da hankali
matukan batun bunkasa ayyukan kere-keren
kamfanonin cikin gida, da kuma tabbatar da
samar da guraben ayyuka ga matasa, domin
bunkasa harkokin tattalin arzikin kasar daga
cikin gida.

Ya ce a kowane lokaci makiya suna amfani da
makamin tattalin arziki ne da nufin raunana
kasar Iran, duk kuwa da cewa bisa himmar
masana da sauran ma'akata masu kwazo, da
kuma taimakon Allah madaukkin sarki,a cikin
tsawon shekaru 37 na juyin Islama, makiya ba
su iya cimma wannan buri nasu ba a kan
jamhuriyar muslunci, a maimakon hakan a
kullum tattalin arzikin kasar na ci gaba da
bunkasa a matsayi na kasa da kasa.

Jagoran ya ci gaba da cewa a bangaren
ayyukan tsaro hakika an samu gagarumin ci
gaba, wanda da taimakon Allah madaukakin
sarki an cimma nasarori masu tarin yawa
bangarori daban-daban na ayyukan tsaro.
Dangane batun zabuka kuwa, jagoran ya ce
babban abin bukata shi ne al'umma su fito
kwansu da kwarkwatarsu a ranar zabe, domin su
zabi abin da su gamsu da shi, wanda shi ne
hakikanin 'yanci da adalci wanda ke tsorata
makiya dangane da damfaruwar al'umma da
juyin Islama.

Tuesday

Hukumar EFCC Ta Damke Wani Shehin Malami




Hukumar EFCC mai yaki da cin hanci a Najeriya ta kama wani mai suna Sheikh Saheed Omoniyi a Garin Ibadan bisa ga laifin zamba


EFCC mai yaki da cin hanci a Najeriya tayi ram da wani mai suna Sheikh Saheed Omoniyi bisa ga laifin zamba cikin aminci inda yake cutar mutane a yanar gizo da sunan cewa shi malami ne na Allah.

Wani Jami’in EFCC na Yankin Kudu ya bayyana haka ga manema labarai a Yau Alhamis. Ayo Oyewole yace Mista Omoniyi mai shekaru 24 ya saba damfarar mutane tun ba yau ba.

Matashin yana yaudarar Jama’a da cewa shine babban Malamin nan na Legas Sheikh Sulaiman Onikijipa.

KU KARANTA: Tambayoyi Hudu Da Dan Aljanna Ne Kadai Zai iya bada Amsarsu

An dai gano cewa wannan matashi yayi sama da kudin Jama’a har fiye da Naira Miliyan 11 inda yake fakewa da sunan wani Babban Shehi, An damke wannan mutumi ne yayin da yake hanyar zuwa Bankin bayan ya damfari wani.