Mukaddashin shugaban kasa Yemi
Osinbajo ya kara tabbatar da cewa
Muhammadu Buhari na nan cikin
koshin lafiya. Osinbajo yace kuma
Buhari zai dawo Najeriya yana
kammala gwajin da yake yi a asibiti.
Osinbaji yayi doguwar waya da
Muhammadu Buhari ya kuma
bayyanawa ‘Yan Jaridan da ke Fadar
shugaban kasar abin da suka tattauna a
wayar. Osinbajo yace sun tattauna ne
game da tattalin arzikin kasa da kuma
batun kasafi da Buhari.
Mukaddashin shugaban kasa Osinbajo
yace ya kuma fadawa Buhari cewa ana
zanga-zanga a kasar inda mutane ke
kuka musamman game da tattalin
arziki. Sannan kuma dai Osinbajo yayi
watsi da rade-radin cewa ana nema a
tursasa ya sauka daga kan kujera, yace
babu wanda ya isa.
A jiya ne aka gudanar zanga-zanga ga
Gwamnatin Buhari saboda halin da ake
ciki a Kasar a halin yanzu. Wani
Babban Jigo Jam’iyyar APC mai mulki
Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yayi kira
ga ‘Yan Najeriyan da su kara hakuri.
@fb.com/HAUSAPOST28
Osinbajo ya kara tabbatar da cewa
Muhammadu Buhari na nan cikin
koshin lafiya. Osinbajo yace kuma
Buhari zai dawo Najeriya yana
kammala gwajin da yake yi a asibiti.
Osinbaji yayi doguwar waya da
Muhammadu Buhari ya kuma
bayyanawa ‘Yan Jaridan da ke Fadar
shugaban kasar abin da suka tattauna a
wayar. Osinbajo yace sun tattauna ne
game da tattalin arzikin kasa da kuma
batun kasafi da Buhari.
Mukaddashin shugaban kasa Osinbajo
yace ya kuma fadawa Buhari cewa ana
zanga-zanga a kasar inda mutane ke
kuka musamman game da tattalin
arziki. Sannan kuma dai Osinbajo yayi
watsi da rade-radin cewa ana nema a
tursasa ya sauka daga kan kujera, yace
babu wanda ya isa.
A jiya ne aka gudanar zanga-zanga ga
Gwamnatin Buhari saboda halin da ake
ciki a Kasar a halin yanzu. Wani
Babban Jigo Jam’iyyar APC mai mulki
Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yayi kira
ga ‘Yan Najeriyan da su kara hakuri.
@fb.com/HAUSAPOST28
No comments:
Write Comments