Malamin dake zaune a garin Zariya ya kuma shawarce su da su yi anfani da iliminsu da kuma sanin da suka yi na sanin yadda shugabanci ya ke, da su zabi ‘yan takara nagari a duk zabukan da za a yi a wannan shekara ta 2019.
Haka zalika Shehin malamin ya kuma yi kira ga duk wani shugaba da wakilai da aka zaba ko kuma da za a zaba, da su rike amanar da aka dora ma su, domin shirin amsa tambayoyin da za a yi ma su a gobe bayan sun sauka daga matsayin da aka zabe su.
Sheikh Malam Abdulhakami Kumasie ya ci gaba da cewar, babbar matsalar da ta ke addabar siyasa a wannan lokaci da ake ciki, shi ne rashin samun shugabanni da kuma wakilai nagari da suke tunanin al’ummar da suke wakilaci da kuma shugabanci.
KU KARANTA : Zaben 2019: Za A Yi Jidali Idan Baki Suka Yi Mana Katsalandan | cewar el-Rufai
A nan ne Malamin addinin musuluncin ya kara da cewar, mafiya yawan wadanda ake zaba a wannan lokaci, da kuma wadanda aka zaba a ‘yan shekarun baya, babu tunanin wadanda suka zabe su, sai dai tunanin kansu a madafun ikon da suke, tun daga jiha ya zuwa tarayya.
Haka zalika Shehin malamin ya kuma yi kira ga duk wani shugaba da wakilai da aka zaba ko kuma da za a zaba, da su rike amanar da aka dora ma su, domin shirin amsa tambayoyin da za a yi ma su a gobe bayan sun sauka daga matsayin da aka zabe su.
Sheikh Malam Abdulhakami Kumasie ya ci gaba da cewar, babbar matsalar da ta ke addabar siyasa a wannan lokaci da ake ciki, shi ne rashin samun shugabanni da kuma wakilai nagari da suke tunanin al’ummar da suke wakilaci da kuma shugabanci.
KU KARANTA : Zaben 2019: Za A Yi Jidali Idan Baki Suka Yi Mana Katsalandan | cewar el-Rufai
A nan ne Malamin addinin musuluncin ya kara da cewar, mafiya yawan wadanda ake zaba a wannan lokaci, da kuma wadanda aka zaba a ‘yan shekarun baya, babu tunanin wadanda suka zabe su, sai dai tunanin kansu a madafun ikon da suke, tun daga jiha ya zuwa tarayya.
No comments:
Write Comments