Showing posts with label labarai. Show all posts
Showing posts with label labarai. Show all posts

Thursday

Open Facebook Account With Invisible Name, Yadda Zaku Bude Fb Account Ba Tare Da Suna Ba.

Barka da warhaka da fatan kuna cikin koshin lafiya.

Yau muna tafe da bayani akan yadda zaku bude FACEBOOK ba tare da suna a jiki ba.

Step 1) Da farko ku bude wannan link http://facebook.com a wayoyinku na android, sannan ku danna Create New Account.


Step 2) Sai ku canja yaren English  Zuwa Yaren Tamil language. Kamar yadda kuke gani a hoton kasa

To Yanzu sai ka nutsu da kyau,, Sannan kabi wadannan steps a nitse , da kuma screen shots  da zaka gani.


1) invisible name fb account text code : wato sunan da zakayi amfani dashi a wajen first name.

 ---->ã‚–ã‚– 💟@() ã‚– ✔<----

Yanzu kayi copy na wannan code dake sama wanda yake tsakani Arrows (between arrows-->__<--) Sai kayi paste a wajen first name.

2) Yanzu sai ka saka lambar wayarka a email box. Kayi amfani da lambar da ba'a taba bude fb account da ita ba. Sannan kar kayi amfani da email, lambar wayarka kawai zaka saka a email box.

3) kayi selecting na Gender.


4) ka cike date of birth.


5) ka cike wajen Password { ka zabi secure password. Wanda yake da capital latter, Lambobi hade da special word kamar su @ $ # : ! ?.}

Step 3) Bayan ka gama ciccikewa sai ka danna Sign Up. Duba wannan screen shot ! 

Bayan ka dannan singup Zasu turoma da Confirmation Code zuwa lamar da ka saka . Sai kayi amfani da code din kayi comfirm na account naka.


BAYAN DUK KAGAMA WANNAN SAI KA MAIDA YAREN YA KOMA ENGLISH.

Ga yadda zakaga sabon account naka wanda ba suna.


Shikenan yanzu ka bude facebook account wanda ba suna a jiki.

Ku cigaba da kasancewa da wannan shafi mai albarka.

Sunday

INEC : YADDA ZA KA DUBA SUNAN KA DA MAZABAR KA A ONLINE .

YADDA ZA KA DUBA SUNAN KA DA MAZABAR KA A ONLINE .


Zaben 2019, Gen Buhari, Dr Atiku


Yau saura kwanaki 2 kacal wa'adin da hukumar zaben Najeriya INEC ta bayar na kowane mai son yin za6e a 2019 ya garzaya maza6ar da yayi rajista domin tabbatar da sunan sa. Tare kuma da kai korafin sa a cibiyar mazabar sa (ward center) idan bai ga sunan sa ba, ko kuma akwai matsala a sunan na sa.

GA DAMA TA SAMU !

Idan ba ka da iko na zuwa mazabar ka domin duba sunan ka, to za ka iya amfani da wayar ka domin duba sunan ka.

Ga yadda abin ya ke :

HANYA TA FARKO

1 - bude manhajar ka ta Opera ko UC Browser sai ka yi bincike ta Google a wannan adireshin :
Voters.inecnigeria.org

Akwai bayanan katin zaben ka da za a nemi ka cike a wannan shafi :

i- sunan jihar ka,
ii- sunan mahaifin ka,
iii- sunan ka,
iv- kwanan watan haihuwar ka (date of birth).

MISALI :
i- KANO
ii- MUHAMMAD
iii- IBRAHIM
iv- 01-10-2000.

KO KUMA :

(i) sunan jihar ka,
(ii) sunan ka (First name),
(iii) lambobi biyar NA KARSHEN VIN ( Voter's Identification Number ) da ke a cikin katin zaben ka, (kana kuma iya sa su gabaki daya).
Sannan ka aika.

MISALI :
i - KANO
ii - IBRAHIM
iii- 01234.

HANYA TA BIYU

2 - ka aika da sunan # Jihar ka, da # Sunan ka, da kuma lambobi 5 na kashe a VIN naka dake a cikin katin zaben ka zuwa ga WANNAN LAMBA :
20120, ko kuma: 08171646879.

MISALI :
KANO
IBRAHIM
01234
zuwa ga 20120, ko 08171646879.

Allah Ya bada sa'a.

A TUNA CEWA KATIN ZABEN KA SHI NE MAKAMIN KA WAJEN FATATTAKAR DUK SHUGABAN BA YA KYAUTATA MAKA, TARE DA ZABEN WANDA KAKE SO YA SHUGABANCE KA.

Allah Ya yi mana zabi mafi alheri. Ameen.

Saturday

Yadda zaku samu Airtel Recharge card Plus 1GB Data *479#

A gaskiya, na buga lambar kuma na samu sako [sms message] daga Airtel cewa ina da kyautar 1GB Data, kuma yana buƙata in sake cajin wasu adadin don buɗe 250MB na mako.

                     Airtel Recharge card Plus 1GB Data *479#

Maganar Gaskiya, bayanin 1GB ba kyauta ba ne. Wasu daga cikcin mutanen mu suna kasa karantawa da kuma fahimtar sakon da aka aika musu  Ta hanyar SMS gare su. amma sai su dinga baza bayanai ba daidai ba. Wannan shine dalilin da ya sa muka rubuta wannan post.

kamfanin Airtel Nigeria subyi amfani da shafinsu na yanar gizo don sanar da tsarin na Airtel Recharge Plus * 479 #. A cikin wannan sakon, zan yi bayanin yadda wannan tsarin yake aiki.


Yadda za a Saita Airtel Recharge Plus 1GB Data a layin wayarka na airtel



Airtel Recharge Plus shi ne sabon tsarin Airtel wanda yake ba ka 250MB kowane mako idan ka sake cajin adadin da ka gani a saÆ™on da aka aika maka bayan ka danna * 479 #. 



 Airtel Recharge card Plus 1GB Data *479#

zaku  dinga samu 250MB a kowane mako, Suna nufin kenen 1GB a wata. Ba za ku iya amfani da wannan 1GB a haka ba, dole ne sai kun yi cajin kudi a layin ku. Bayan kunyi
chajin kudin ne zasu baku damar amfani da wannan Data 1GB , Wanda zaku samu 250MB a duk sati [mako].



Domin bude wannan free 1GB data,sai kayi chajin kudi dai-dai da adadin da kuka gani a saƙon da Airtel suka aika muku ta hanyar SMS , bayan danna *479# don buɗe Wannan 250MB a duk mako.

Thursday

Bidiyo : Wata mata ta kashe mijinta ta yi yunkurin kone gawarsa.

Wani ma'abocin amfani da dandalin sada zumunta  ya yada labarin wata mata da ta kashe mijinta sannan ta saka wa gawarsa wuta bayan sun yi wani kazamin fada.
na Facebook

A cewar wanda ya yada labarin, lamarin ya faru ne a jihar Bayelsa, sannan ya kara da cewa lamarin ya jawo hankalin makwabtan ma'auratan wadanda suka kira 'yan sanda. Ya kara da cewa, jami'an 'yan sanda sun zo sun dauki gawar mijin sannan sun tafi da matar.

Ko a kwanakin baya wata Mata ta yi yunkurin Kashe Mijinta Ta Hanyar Burma Masa Wuka A Ciki Saboda Zai Yi Mata Kishiya Ana zargin wata mata mai suna Amina Banaga Maru dake garin Gusau babban birnin jihar Zamfara da niyar hallaka mijinta ta hanyar soka masa wuka a ciki har sau uku.

Lamarin wanda ya auku a RANAR Litinin, 24 ga watan Yuni, bincike ya nuna cewa matar ta yi niyar halaka mijin nata ne saboda tsantsar kishi. Bayanan da muka samu sun tabbatar mana da cewa ana zargin Amina ta yi wa mijin nata wannan danyen aikin ne saboda niyyar da yake da ita na yi mata kishiya.

GA BIDIYON NAN KASA


Wednesday

Yadda mutanen Najeriya za su ba Duniya mamaki – Cewar Osinbajo

Rahotanni sun zo mana cewa mataimakin shugaban kasar Najeriya, Yemi Osinbajo, ya bayyana cewa irin kokarin da mutanen kasar nan su ke yi a fannin fasaha, ya na iya ci da kasar gaba. Farfesa Yemi Osinbajo ya ke cewa irin kwazon ‘Yan Najeriya ya na iya zama sanadiyyar kawowa kasar mafita a kan matsalolin fasaha na zamani da za su sa Najeriya ta rikide a sahun Duniya. 

Mataimakin shugaban kasar ya bayyana wannan ne a lokacin da ya yi wani zama da wasu kwararru a kan harkokin kasar waje da masu zuba hannun jari a Najeriya a Birnin New York na Amurka. Babban hadimin mataimakin shugaban kasar watau Laolu Akande ya ke cewa, Osinbajo ya bayyana wannan ne a lokacin da a ka jefe sa da wasu tambayoyi kan rikicin fasahar Duniya.

Osinbajo ya ce: “Ba mu son wani rikici a halin yanzu. Mu na maraba da duk wani kamfani da zai zo kasuwanci Najeriya. Huawei su na Najeriya yanzu haka tare da wasu manyan kamfanoni.” 

KU KARANTA: Gwamnan Yobe zai aika ‘Dalibai zuwa karatu a kasar waje

 “Ba mu kai ga yanke shawara a game da sha’anin fasahar 5G ba. Idan a na maganar fasaha, sai mu tambaya ta ya kasar Sin su ka kai ga haka? Ta ya sauran jama’a su ka yi nisa? Mu ma za mu kai ga haka da kan mu.” 

Mataimakin shugaban kasar ya cigaba da cewa gwamnatin Najeriya za ta yi amfani da baiwar da Ubangiji ya yi wa Matasan Najeriya wajen cin ma burin kasar.

Wannan zai sa kasar ta yi zarra a ban kasa. “Mu na da kasuwar wayar salula na sama da mutane miliyan 174 a Duniya. Najeriya na cikin manyan kasuwannin salula 10 a ban kasa.” Inji Osinbajo.

 Ya cigaba da cewa: “A Duniya, mu ne na 2 a Duniya wajen kasuwanci ta yanar guzo, bugu-da-kari akwai ‘yan Najeriya miliyan 17 da ke amfani da Facebook.
“Kamfanin Microsoft sun yi alkawarin kafa cibiya ta Dala miliyan 100 a Najeriya domin Nahiyar Afrika.” kamar yadda Laolu Akande ya bayyana a jawabin na sa.

SOURCE LEGIT.NG 

Tuesday

Ba za'a dauki lokaci mai tsayi wajen bayyana sunayen minstoci ba : shugaba Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi magana a game da shirin kafa gwamnatinsa a Najeriya. Hakan na zuwa ne bayan kusan wata guda da shugaban kasar ya sake darewa kan karagar mulki.

Shugaba Buhari ya yi wannan magana ne ta bakin babban Hadiminsa, Femi Adesina, wanda ya ce a wannan karo, shugaban kasar ba zai dauki dogon lokaci wajen fitar da sunayen Ministocinsa ba.

Femi Adesina ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya yi wata doguwar hira da Mujallar Interview Magazine. Mista Adesina ya yi wannan jawabi ne a Ranar Litinin dinnan, 24 ga Watan Yuni, 2019. A 2015, shugaban kasar ya dauki kusan rabin shekara ba tare da ya kafa gwamnati ba.

Wannan ya jawo jama’a su ka fara kiransa ‘Baba Go Slow’ watau da Hausa "Uban Masu nawa a Najeriya!"

DUBA WANNAN : Kwana Casa'in - Kashi Na Sha biyu 12 - AREWA24 

Da a ka tambayi Adesina game da lokacin da za a nada manyan mukarrabai a gwamnatin Buhari, sai ya ce jama’a ba za su kara kwana guda na lokacin da bai zama dole ba wajen jiran Ministoci. Mista Adesina ya ce: “Shi kan sa shugaban kasa ya fada da bakinsa cewa wannan karo ba za a jima wajen kafa gwamnati kamar yadda a ka yi a 2015 ba, dalili kuwa saboda yanayin ba daya ba ne.”

A wancan lokaci a wa’adin farko, fadar shugaban kasar ta kowa da cewa an samu bacin lokaci wajen mikawa gwamnati mai zuwa wasu takardu wanda hakan ya yi sanadiyyar dadewar da a ka yi. Idan ku na biye da mu, ku na da labari cewa har yanzu babu wadanda shugaban kasa ya nada face Akanta Janar na kasa da kuma shugaban kamfanin NNPC tun da ya zarce a kan mulki a Watan Mayu.

Monday

Yanzu Yanzu: Masu ruwa da tsaki a APC sun mamaye fadar Shugaban kasa. : HOTUNA

Sun yi kira ga shugaba Buhari da ya ja jirgin yan Najeriya sannan ya cika alkawaran da ya daukar ma yan Najeriya.

 Mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) karkashin inuwar Concerned APC National Stakeholders (CANS) sun yi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya dakatar da da Abba Kyari, Shugaban ma’aikatan Shugaban kasa. Domin matsin lamba kan bukatarsu, mambobin CANS sun mamaye fadar Shugaban kasa a ranar Litinin, 24 ga watan Yuni.

Musamman suka bukaci Shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya karbi ragamar gwamnatinsa daga hannun na kewaye dashi yayinda ya fara mulki a zango na biyu, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wasu daga ciki allunan da suka dauka na dauke da rubutu daban-daban kamar 'Ya zama dole Abba Kyari ya tafi', 'Ya zama dole PMB ya karbi ragamar mulki', 'Muna son sabbin shawarwari ba na tsoffin da suka shafe sama da shekaru 40 a mulki ba', da kuma 'Ya zama dole a karrama kwazo aiki'da dai sauransu.

Masu ruwa da tsaki a APC sun nemi Buhari ya dakatar da Abba Kyari Source: UGC

KU KARANTA KUMA: Yanzu-yanzu: Kotun zabe ta yi watsi da bukatar Atiku da PDP na duba na'urara zabe na INEC  

Kungiyar tace cewa yan Najeriya sun zabi shugaba Buhari ne ba wai Mamman Daura, Ismail Funtua ko Abba Kyari ba Source: UGC Dr Symeon Chilagorom, jagoran kungiyar yayi korafin cewa yan Najeriya sun zabi shugaba Buhari ne ba wai Mamman Daura, Ismail Funtua ko Abba Kyari ba. Sun bukaci Buhari ya karbi ragamar mulki Source: UGC Ya jadadda cewa yan Najeriya ba za su lamunci abunda ya faru a karo na farko ya sake maimaita kansa ba.

DUBA WANNAN : Kwana Casa'in - Kashi Na Sha biyu 12 - AREWA24  

SOURCE LEGIT.NG

Yanzu-yanzu: Kotun zabe ta yi watsi da bukatar Atiku da PDP na duba na'urara zabe na INEC

Kotun shari'ar zabe shugaban kasa ta yi watsi da bukatar jam'iyyar Peoples Democratic (PDP) da dan takararta, Atiku Abubakar, na duba na'urar hukumar gudanar da zabe ta kasa mai zaman kanta INEC.

A hukuncin, kwamitin alkalai biyar sun yi ittifakin cewa ba zai yiwu a amsa bukatar PDP ba saboda an kai ruwa rana kan shin hukumar INEC ta yi amfani da yanar gizo wajen tattara sakamakon zaben shugaban kasa. Channels TV ta bada rahoton cewa alkalan sun bayyana cewa ba zai yiwu sun sanya baki cikin al'amarin ba a wannan lokaci.

KARANTA KUMA : Amurka ta kai wa Iran hari, ta lalata musu makaman yaki  

 Lauyan Atiku da PDP, Levy Uzokwu, ya bukaci kotun zaben ya wajabtawa INEC ta basu daman bincike cikin yanar gizo da na'urar 'Card Reader' da akayi amfani da su lokacin zabe. Amma lauyan INEC, Yunus Usman, ya bukaci kotu tayi watsi da wannan bukata inda yace: "Suna tambayarmu mu basu abinda bamu da shi,"

Ya kara da jawo hankalin kotun da bukatar da PDP ta gabatar ranar 6 ga Maris cewa kayyayakin zabe kawai ta bukaci gani ba yanar gizo ba Jam'iyyar PDP da Atiku Abubakar na kalubalantar nasarar shugaba Muhammadu Buhari na APC a zaben shugaban kasan da ya gudana ranar 23 ga Febrairu, 2019.

SOURCE LEGIT.NG

Sunday

Amurka ta kai wa Iran hari, ta lalata musu makaman yaki

Wasu rahotanni daga Amurka sun bayyana cewa kasar ta kai wani hari ta yanar gizo (internet) a kan kwamfutocin da dakarun soji na juyin-juya hali a kasar Iran ke amfani da su wajen sarrafa manyan makaman yaki da suka hada da makamai masu linzami (nukiliya).

Rahotanninsun bayyana cewa an ai harin ne a ranar Alhamis bayan shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya canja ra'ayinsa a kan kai hare-hare a wasu wurare mallakin kasar Iran.

Harin da Amurkan ta kai ba zai rasa nasaba da harbo wani jirgin yakin kasar Amurka mai amfani da na'ura da kasar Iran ta yi ba a cikin makon jiya da kuma wani harin da aka kai wa jiragen dakon danyen man fetur na Amurka, wanda ta dora alhakin kai harin a kan kasar Iran.

Babu wata kafar watsa labarai wacce ba ta Amurka ba da ta bayar da tabbacin cewa harin ya lalata makaman yakin kasar Ira.
Shugaba Trump dai ya bayyana cewa kasar Iran ta tafka babban kuskure da ta harbo jirgin yakin kasar Amurka da ake sarrafa wa da na'ura.

Jirgin, maras matuki, da Iran ta harbo na daga cikin jiragen yaki masu matukar tsada da kasar Amurka ta mallaka.

DUBA WANNAN: Yadda 'yan sanda suka yi wa wasu masu garkuwa da mutane dirar mikiya a mafakarsu. ðŸ”—

Trump ya bayyana cewa zai shafe kasar Iran daga doron kasa idan yaki za su yi.
Wutar yaki da ke ruruwa tsakanin kasashen biyu ta jawo zaman dar-dar a kasashen yankin Persia.

Tuni Andrew Murrison, sakataren harkokin kasashen waje na kasar Birtaniya ya isa kasar Iran domin tatauna wa da shugabannin kasar domin yi musu sulhu da kasar Amurka.

Shugaba Trump ya bayyana cewar a shirue yake ya yi sulhu da kasar Iran tare da bayyana cewar kasar Amurka a shirye take idan kasar Iran yaki take so su gwabza. Sai dai, ya gargadi kasar Iran da ta sani cewa Amurka ba tsarar ta ba ce.

POSTED BY LEGIT.NG

DUBA WANNAN KUMA.

Yadda Ake Dawo da Lambar WhatsApp Idan ta Daina Aiki

Yadda zaku maida lambar wayar ku zuwa ta kasashen waje. in 5min

Yadda Zaku Bude Facebook Account Ba Tare Da Suna Ba.

Yanda Zaka Samu Rancen Kudi Har N100,000 A Layin Etisalat New(9mobile)  

Yadda Ake Connecting Na Android Xender Da Computer. : Android Tutorial 2020. 

Ko kuma Ku ziyarci Page namu mai tâken YADDA AKE....🔗🔗

Yadda 'yan sanda suka yi wa wasu masu garkuwa da mutane dirar mikiya a mafakarsu.

Rundunar 'Yan sandan Jihar Neja ta gano wasu gidaje da masu garkuwa da mutane don karbar kudin fansa suke amfani da su a matsayin mafaka a jihar. The Nation ta tabbatar da cewa an gano uku daga cikin gidajen a unguwar Bosso da ke Minna sakamakon bayyanan sirri da mazauna unguwar suka bawa bawa 'yan sanda. Tuni dai 'yan sandan sun rufe gidajen.

Majiyar Legit.ng ta gano cewa an kama mutane bakwai da wasu bindigu kirar AK 47 yayin da 'yan sandan suka kai sumame a gidajen. A halin yanzu 'yan sandan ba su bayar da cikaken bayani kan abinda ke faruwa ba.

DUBA WANNAN: Yanzu Yanzu: Jirgin sama ya kwace ya shiga jeji yayin sauka a Fatakwal ; Hotuna   

A yayin da aka tuntube shi, Mai magana da yawun 'Yan sandan jihar, Abubakar Muhammad ya ce baya gari saboda haka ba zai iya bayar da wani bayannai ingantattu kan gidajen da aka gano ba. Ya kuma ce duk wani bayani da aka bayar a yanzu kan gidajen zai iya kawo cikas ga binciken duba da cewa ba a kammala binciken ba.

Kakakin 'yan sandan ya ce zai bawa manema labarai cikaken bayani da zarar an kammala binciken. Kwamishinan 'Yan sandan jihar, Adamu Usman ya shaidawa wasu manema labarai cewa suna kawo tangarda ga binciken inda ya gargadi su da zuwa kusa da gidajen. Sai dai makwabta gidajen da ke aka rufe sun tabbatar da cewa 'yan sanda sun kai sumame gidan kuma an kama wani adadin mutane.

SOURCE LEGIT.NG

Saturday

Yanzu Yanzu: Jirgin sama ya kwace ya shiga jeji yayin sauka a Fatakwal ; Hotuna

Wani jirgin sama na kamfanin Air Peace ya ketare titin sa a filin tashi da saukan jirage na Fatakwal da ke jihar Rivers yayin da ake ruwan sama da bakin kwarya.


A cewar daya daga cikin fasinjan da ke jirgin, lamarin ya faru ne a yayin da jirgin ke sauka a filin saukan jiragen.


Fasinjojin jirgin Air Peace yayin da ake tallafa musu fitowa daga jirgin da ya shige daji a Fatakwal .

DUBA WANNAN : Rikici : Iran ta tarwatsa Jirgin leÆ™en Asiri na Amurka.  

Jirgin ya yi birki a cikin daji kimanin mita 200 daga titin sa. Wani shaidan ganin ido ya ce an fitar da dukkan fasinjojin da ke cikin jirgin an koma da su wurin da ya dace jirgin ya tsaya tun farko.

Fasinjojin jirgin Air Peace yayin da ake tallafa musu fitowa daga jirgin da ya shige daji a Fatakwal Source: legit.ng.

Friday

Rikicin jam'iyya: Ana fargabar za a sake dakatar da wani gwamnan APC

Akwai yiwuwar rikicin da ya kunno kai a jam'iyyar APC reshen Jihar Edo sai iya sanadin dakatar da Gwamna Godwin Obaseki

Sai dai magoya bayansa suna ganin gwamnan yana iya samun wata mafita kafin zaben 2020 a jihar

A bangarenta, Jam'iyyar APC ta kasa ta yi tir da irin Obaseki da Bala Mohammed na Bauchi kan ikirarin magudin da aka ce an yi wurin zaben shugabanin majalisar dokokin jihar.

Akwai alamun cewa Jam'iyyar All Progressives Congress (APC) za ta dakatar da Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo kamar yadda ta dakatar da Gwamna Abdulaziz Yari na jihar Zamfara.

Wasu hadiman gwamnan biyu sun shaidawa Legit.ng a ranar Juma'a 21 ga watan Yuni cewa suna juyayin abinda zai faru da gwamnan duba da cewa rikicin jam'iyyar APC na jihar yana daukan sabon salo.

A cewarsu, rikicin da ke tsakanin Obaseki da mai gidansa wata shugaban jam'iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole zai iya janyo wa jam'iyyar matsala a zaben gwamna mai zuwa.

DUBA WANNAN: Da duminsa: Ala tilas, Ahmad Lawan ya sallami makiyin Buharin da ya ba mukami. 

"Kamar yadda Cif John Odigie-Oyegun ya fadi a baya-bayan nan, muna fargabar rikicin zai iya janyo wa APC shan kaye a jihar. Sai dai gwamnan ya dauki wannan matakin ne saboda ya gaji da katsalandan da ake masa dama sama," inji daya daga cikin hadiman gwamnan a hirar tarho da akayi dashi.

Da ya ke amsa tambaya kan dalilin da yasa gwamnan ya yi zaben 'yan majalisun da ake ganin ya sabawa ka'ida, wani hadimin gwamnan ya ce wannan ba abin damuwa bane saboda Obaseki ya aikata abinda ya ke ganin shine dai-dai duba da yadda wasu ke shirin tayar da tarzoma a jihar.

A bangarenta, Hedkwatan Jam'iyyar APC na kasa ta yi wa Obaseki da Bala Mohammed kaca-kaca kan abinda da ta kira rashin bin ka'ida wurin zaben shugabannin majalisun dokokin jiha a Edo da Bauchi.

Jam'iyyar ta ce zaben shugabannin majalisun da aka yi cikin sirri abin kunya ne ga demokradiyya inji Kakakin jam'iyyar na kasa Mallam Lanre Issa-Oniliu.

SOURCE LEGIT.NG

Da duminsa: Ala tilas, Ahmad Lawan ya sallami makiyin Buharin da ya ba mukami

A ranar Alhamis shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya sallami sabon hadimin da ya nada, Festus Adebayo, bayan koke-koken masoyan shugaba Buhari da yan jam'iyyar APC kan ta wani dalili zai nada sanannen makiyin Buhari.

Nadin Festus Adebayo, ya tayar da hankalin masoya Buhari musamman a kafar ra'ayin da sada zumunta ta Tuwita inda aka kunnawa sanata Ahmad Lawan wuta kan nadin dan jaridan da ya dade yana yiwa jam'iyyar APC adawa.

A jawabin da mai magana da yawun Ahmad Lawan ya saki, Mohammed Isa, ya bayyana cewa shugaban majalisar dattawan ya janye nadin da ya yiwa Festus Adedayo kuma fatan alkhairi.

KU KARANTA: Nadin mukamai: Aisha ta kara kwaba wa Buhari magana a fakaice.

Jawabin yace: "Ofishin shugaban majalisar dattawa ta janye nadin da ya yiwa Mista Festus Adedayo matsayin hadimin shugaban majalisa kan yada labarai kuma an sallameshi, yana yi Mista Adebayo fatan alheri a rayuwarsa."

Mun kawo muku rahoton cewa kungiyar Matasa masu ruwa da tsaki jam'iyyar APC a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangan nuna rashin jin dadin ta kan nade-naden da Shugaban Majalisar Dattawa yayi.

A yayin da ya ke jawabi ga matasan jam'iyyar da ke zanga-zanga, sakataren yada labarai na kasa, Abuh Andrew ya bukaci Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmed Lawan ya sake bita kan nade-naden da ya yi domin ya samu karbuwa ga dimbin matasan jam'iyyar.

SOURCE LEGIT.NG

Thursday

Nadin mukamai: Aisha ta kara kwaba wa Buhari magana a fakaice

Aisha Buhari, uwargidan shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ta kara caccakar gwamnatin mijinta, wannan karon a kan nadin mukamai a gwamnatinsa.


Ta saka wani faifan bidiyo a shafinta na Tuwita inda wani dan gani kashenin Buhari a Tuwita (@ayourb) ya koka a kan yadda shugaban kasar ke bawa mutanen da basu yarda da akidansu ba mukami.

A cewar sa, " idan shugaba zai bayar da mukamai a gwamnati, yana bawa mutanen da suka yarda da akidansu ne, mutanen da zasu taimaka masa wajen kawo canjin da gwamnatinsa ke burin gani, ba haka kawai yake bayar da mukamai ga kowa ba. 

Ta yaya zaka bawa masu yakar akidar ka mukami kuma ka yi tunann zasu taimaki gwamnatin ka ta cimma burin ta ?

DUBA WANNAN: Rikici : Iran ta tarwatsa Jirgin leÆ™en Asiri na Amurka. 

" Ko da mutane basu ji haushin ka a kan bawa masu sukar ka mukami ba, ya kamata mu fada maka cewa mutanen da ka ke dauka domin su taya ka aiki basu yarda da akidun ka ba balle manufofin gwamnatin ka ."

Da take kara yada wannan sakon faifan bidiyo na @ayourb, matar shugaban kasar ta ce, " ba zaka iya kawo canji da mutanen da basu yarda da ajendar ka ba...ta ya ya zaka samu damar cimma manufar ka idan ka nada mutanen dake yakar manufofin ka ."

Rikici : Iran ta tarwatsa Jirgin leƙen Asiri na Amurka.

Da safiyar Alhamis, 20 ga watan Yuni, 2019 Kasar Iran ta baro jirgin leken asirin kasar Amurka yayinda rikici ke cigaba da kunno kai tsakanin manyan kasashen guda biyu.



Yayinda jami'an tsaron kasar Iran na ikirarin cewa jirgin Amurkan ta shiga huruminta shi yasa suka barota, amma jami'an Amurka sun ce ba haka bane, jirgi bata shiga hurumin Iran ba a lokacin.
Har yanzu ba'a menene gaskiya lamarin ba.

KU KARANTA: Daga karshe : An Yanke shawarar korar Abdul-aziz Yari daga Jam'iyyar APC. 

Shafin labaran jihar Hormozgan tace:
"Mun baro jirgin leken asirin kasar Amurka. Mun barota ne lokacin da ta shigo hurumin kasar Iran kusa da Koumobarak."

Wannan abu da ya faru shine fito-na-fito na farko tsakanin Iran da Amurka yayinda aka fara cacan baki tsakanin kasashen guda biyu tun hawan mulki shugaba Donald Trump da sanyawa Iran takunkumi.
Amma kasar Amurka ta karyata rahoton Iran cewa an shiga huruminta.


Daya daga cikin abubuwan da sojojin Amurka suka gano a yankin.

Kakakin hukumar sojin Amurka, Bill Urban, yace : "Babu wani jirgin leken asirin da ya shiga hurumin Iran."

Kwamandan hukumar tsaron Iran ya ce wannan abu da kasar tayi sako ne ga kasar Amurka.

Janar Hossein Salami yace Iran ba tasa wani niyyar yaki da wani kasa amma fa shirye take da gwabzawa da kowa.


Wednesday

Daga karshe : An Yanke shawarar korar Abdul-aziz Yari daga Jam'iyyar APC

Kwamitin da Jam’iyyar APC ta nada domin bin diddigin matsalolin da jam’iyyar ta fada da kuma mummunar kayin da ta sha a zaben 2019 ta mika rahoton ta.

Kwamitin ta ce irin yadda tsohon gwamnan jihar AbdulAziz Yari ya ja ragamar jam’iyyar na daga cikin babban dalilin da ya sa aka yi ta samun matsaloli a jam’iyyar da ya kai ga har ta sha kasa a zabukkan a aka yi a baya.

KU KARANTA WANNAN :- Kwana Casa'in - Kashi Na Sha daya 11 - AREWA24  

Baya ga shi, kwamitin ta ce ta samu rahotannin yankan baya da mataimakin jam’iyyar APC na kasa reshen Arewa, Sanata Lawal Shuaibu ya rika yi wa jam’iyyar.

sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara, Mohammed Bakyasuwa ne yayi wannnan bayani da yake zantawa da manema labarai a Abuja.

” Ina so kowa ya sani cewa tsakanin mu da ‘yan bangaren tsohon gwamna Yari ba’a ga maciji yanzu domin kuwa anja layi. Yari ne shafaffen da ya jefa jam’iyyar mu cikin matsalolin da muka fada a yanzu.

” Yanzu dai mun dauki matsaya daya dukkan mu cewa daga yau, mun kori AbdulAziz Yari a APC, da Sanata Lawali shu’aibu. Kowa ya sani kuma wannan shine matsayar mu ‘yan jam’iyyar APC na Zamfara.

Idan ba a manta ba an yi ta kai ruwa rana tsakanin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara a lokacin zaben fidda gwani na ‘yan takarar jam’iyyar a zaben 2019 da a karshe wannan matsala da suka rika samu ya kai su ga fadawa a zabukan da aka yi.

Kotun koli ta kori dukkan wani dan takara na APC daga jihar Zamfara bayan kara da sanata Kabiru Marafa ya shigar .

A karshe dai APC ta tashi a tutan babu wadda ko dan majalisar jiha daya bata iya samu ba saboda sakaci da handamar tsohon gwamna Yari.

SOURCE PREMIUMTIMES-HAUSA

Tuesday

Kuma dai: Ganduje ya kafa kwamiti domin sake duba rahoton hukumar yaki da rashawa kan sarkin kano

Gwamna Ganduje ya kafa wata kwamiti domin ta sake duba rahoton hukumar yaki da rashawa kan Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II .
Gwamna ganduje

Da farko hukumar sauraron kurafe-korafe da yaki da rashawa tace ta gano sama da naira biliyan 3.4 da aka yi almubazaranci dashi a karkashin Sanusi - An tattaro cewa anyi almubazaranci da kdin ne a tsakani 2014 da 2017 Gwamnatin jihar Kano ta kafa kwamiti don sake duba ga rahoton hukumar sauraron kurafe-korafe da yaki da rashawa na jihar kan zargin almubazaranci da masarautan Kano tayi da kudi har kimanin naira biliyan 3.4.

Wata majiya ta gidan Gwamnatin Kano ta bayyana ma jaridar Daily Trust cewa an kaddamar da kwamitin ne a ranar Juma’a a sannan kuma an bukaci hukumar da ta fara gudanar da aiki ba tare da bata lokaci ba. A cewar majiyar, wasu mutane daga gwamnatin cikin gida da na waje sun matsa ma gwamnan lamba da ya bari hukumar ta gudanar da aikinta yanda ya kamata.

“A wannan lamarin, hukumar tana iya cigaba da gudanar da bincikenta kuma maiyiwuwa binciken zai iya kai ga dakatar da sarkin kamar yanda hukumar ta bukaci ayi a baya." 

KU KARANTA KUMA: Kwana Casa'in - Kashi Na Sha daya 11 - AREWA24 

Majiyar tace, “Ga dukkan alamu, gwamnatin bata yi marhaban da martanin da sarkin ya mayar ga wasikan da aka tura masa ba, saboda wannan dalilin ne aka kafa kwamitin.”

Zaben 2019: Daga karshe Jega yayi magana akan rigimar na’urar INEC

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya musanta gabatar da jawabi akan samuwar na’urar ajiye sakamakon zabe a lokacin da ya shugabanci hukumar.

Farfesa Jega a wani sharhi da aka yada a kafofin watsa labarai, an rahoto inda yake cewa hukumar INEC na da na’urar ajiye sakamakon zabe kuma ‘tana aiki,’ ko a lokacinsa.

A wani sakon wasikar waya ga Premium Times ta hannun wani hadiminsa, Farfesa Jega ya musanta bayar da jawabin, inda yake bayyana hakan a matsayin ‘kalaman ganganci.’

KU DUBA KUMA: Kwana Casa'in - Kashi Na Sha daya 11 - AREWA24

Ya bayyana cewa hukumar a karkashin jagorancinsa bata taba aika sakamakon zabe ta na’ura ba.

Duk da musanta lamarin da Farfesa Jega yayi, rigima akan na’urar INEC na cigaba da kewaye kasar.

Hukumar INEC duk da haka ta dage cewa bata yi amfani da na’ura ba wajen aika sakamakon zaben 2019 ba, inda ta alakanta lamarin da jinkiri da aka samu wajen sakin kasafin kudin hukumar na 2019.

Solomon Soyebi, daya daga cikin kwamishinonin INEC na kasa a ranar Litinin, 17 ga watan Yuni, yace sabanin cece-kuce da yamadidi da ake yi, hukumar bata aika sakamakon zaben shugaban kasa na 2019 zuwa na’urarta ba.

Haka zalika, yace hukumar INEC tayi gwajin na’uran wajen aika sakamakon zabe a zabukan Anambra, Sokoto da Osun da aka gudanar kafin zabukan 2019, inda ya karfafa cewa ba ayi amfani da fasahan ba a zaben 2019.

SOURCE LEGIT.NG

Monday

Yadda Mohammed Morsi ya yanke jiki ya fadi matacce a kotu

Tsohon shugaban kasar Misra (Egypt), Mohammed Morsi, da sojoji suka yi wa juyin mulki a shekarar 2013, ya mutu a kotu, kamar yadda gidan Talabijin na kasar ya rawaito.

Sashen Turanci na jaridar BBC ya rawaito cewar Morsi ya suma a cikin kotu inda ake tuhumarsa da aikata laifin satar muhimman bayanan sirri (Espionage). Shekarunsa na haihuwa 67.

An hambarar da gwamnatin Morsi bayan shekara daya da hawansa mulki biyo bayan wata zanga-zanga mai zafi.

Tun bayan lokacin yake tsare a kotu.
Morsi ne zababben shugaban kasar Misra na farko, ya hau mulki ne bayan an tursasa tsohon shugaban kasar, Hosni Mobarak, yin murabus.

Bayan an tunkude Morsi daga kan mulki, hukumomin kasar Misra sun shiga farautar magoya bayansa da 'yan kungiyarsa ta 'yan uwa Musulmi (Muslim Brotherhood).

Sunday

Katsina : Akwai Alamun Nasara , PDP ta maka gwamna masari a kotu : Cewar Lauyan PDP

A cigaba da sauraran qarar da jam’iyyar PDP ta shigar a gaban kotun sauraran qararakin zave da ke Katsina an fara gabatar da shaidu dangane da rashin ingancin zavan gwamnan da ya gabata wanda jam’iyyar PDP ta yi zargin an tafka maguxi.
aminu bello masari, lado dan marke

Sanata Yakubu Lado danmarke na jam’iyyar PDP suka shigar da qarar inda suke qalubalantar nasarar da gwamna Aminu Bello Masari ya samu wanda hakan ya qara tabbatar da shi a matsayin zavavan gwamna a karo na biyu a qarqashin jam’iyyar APC.

DUBA WANNAN : Sunayen Tsaffin gwamnonin APC 3 da Buhari zai nada ministoci.  
Sai dai lauyan da ke jagorantar wannan shari’a a vangaran jam’iyyar Adawa ta PDP Gordy Uche ya bayyanawa manema labarai cewa bisa ga yadda suke ganin wannan shari’a na tafiya akwai alamu nasara so sai. “Muna da qyaqqyawar fatan cewa za a samu nasara kai tun daga ranar da muka shigar da wannan qara muke da qyaqqyawar fatan cewa akwai nasara a wannan shari’a da ake yi kuma za a samu canji na yi maku alqawarin cewa zaku ga canji ba da jimawa ba”. Inji Gordy Uche 

Lauya ya qara da cewa akwai abubuwa mahimahimcin a wannan shari’a da ya kama jama’a su sami wanda da shi ne suke sa ran za su samu nasaraa wajan wannan shari’a ake fafatawa.

 “Abu mai matuqar mahimmacin da nake so a sani shi ne, Bangaran da wannan qara ta ya shafa wanda yake da mahimmanci a garemu, wanda kuma muke yawan nanawa tun lokacin da muka shigar da wannan qarar shi ne, wanda muke qara wato gwamna Aminu Bello Masari baya da cikakkun takardun ilimi da ya kamata ya tsaya takarar gwamnan jihar Katsina” inji shi. 

Sai dai kuma da muka tuntuvi vangaran gwamnati wanda sune aka yi qara domin jin martanin da za su maida dangane da wannan batu na rashin cikakun takardun shaidar Ilimi da suke zargin gwamna Masari. Xaya daga cikin jagorarin wannan shari’a a vangaran gwamnati Ernest Obunidike ya ce wanda muke karewa yana da takardun yin takarar gwamnan jihar Katsina kuma ya yi takara ya ci zave ya sake yi ya ci zave saboda haka ya cancanta.

Ya qara da cewa “Abu na biyu shi ne ba mu da buqatar yin musayar maganganu da lauyan wanda ya yi qara saboda maganar tana gaban kotu har yanzu, idan har gaskiya ne zargin da suke yi su kare shi a gaban kotu amma ba za mu yi masanyar kalamai da su ba tukuna”. 

Wannan shari’a dai na cigaba da xaukar hankali musamman yadda aka zargin cewa xan takarar jam’iyyar PDP Sanata Yakubu Lado Xanmarke ya sayar da takarar ta sa tun kafin zave zargin da ke neman ya zama shafa labari shuni.

SOURCE Leadershiphausa