Showing posts with label taskar hausa film. Show all posts
Showing posts with label taskar hausa film. Show all posts
Wednesday

Film Trailer : "LABARINA" Staring:- Nafisa Abdullahi Nazir Sarkin waka
Film Trailer : "LABARINA" Staring:- Nafisa Abdullahi Nazir Sarkin waka
Wannan wani kayataccen shiri ne wanda haziki fasihin mai bada umurni Aminu saira yayi Film mai sunan 'Labarina'.
Wanda a ciki yake dauke da manya manyan jarumai:-
1. Nafisa Abdullahi
2. Hafsat Barauniya
3. Nuhu Abdullahi
4. Nazir M Ahmad sarkin waka
Da dai sauransu
CHECK MORE 🌏
@Arewasound
Friday

Yadda Rikici ya barke Tsakanin Matan Kannywood Biyu - Akan Dino Melaye
Duka 'yan matan sun yiwa Sanatan waka da fasta ta siyasa sun kai masa, inda ya dauki hoto da kowaccen su.
Wani rikici da ya barke tsakanin matan Kannywood guda biyu Teema Makamashi da Fati Mohammed, inda suke rikici akan Sanatan jihar Kogi ta Yamma Sanata Dino Melaye.
Rikicin ya samo asali ne lokacin da Teema Makamashi take gargadin Fati Mohammed akan kwaikwayenta da tayi wurin yiwa Sanatan waka.
Wata sabuwa: Rikici ya barke tsakanin matan Kannywood biyu akan soyayyar Sanata Dino Melaye
Ga abinda Teema Makamashi ta rubuta a shafinta na Instagram:
"Keda samun soyayyarsa sai dai ki gani daga nesa"
Tauraruwar Teema Makamashi wacce ita ce ta fara yiwa Sanata Dino Melaye waka, tayi wannan habaicin ne ga Fati Mohammed wacce ta kwafeta.
KU KARANTA: Bidiyo da hotuna : Bikin shan rantsuwar shugaban kasa da mataimakinsa.
Teema tayi rubutun ne a shafinta na Instagram inda ta cigaba da cewa, "Ga wani sabon salon shima idan zaki yi, banda waka, tunda kome nayi sai kinyi, kina tare da bakar wahala indai ni zaki dinga kwaikwaya."
Tauraruwar ta saka hoton fastar siyasa da tayi wa Sanatan a shafinta na Instagram a lokacin da tayi wadancan habaicin.
An ga Fati Mohammed ta yiwa Sanata Dino Melaye waka da kumaa fasta ta siyasa.
SOURCE LEGIT.NG
Wani rikici da ya barke tsakanin matan Kannywood guda biyu Teema Makamashi da Fati Mohammed, inda suke rikici akan Sanatan jihar Kogi ta Yamma Sanata Dino Melaye.
Rikicin ya samo asali ne lokacin da Teema Makamashi take gargadin Fati Mohammed akan kwaikwayenta da tayi wurin yiwa Sanatan waka.
Wata sabuwa: Rikici ya barke tsakanin matan Kannywood biyu akan soyayyar Sanata Dino Melaye
Ga abinda Teema Makamashi ta rubuta a shafinta na Instagram:
"Keda samun soyayyarsa sai dai ki gani daga nesa"
Tauraruwar Teema Makamashi wacce ita ce ta fara yiwa Sanata Dino Melaye waka, tayi wannan habaicin ne ga Fati Mohammed wacce ta kwafeta.
KU KARANTA: Bidiyo da hotuna : Bikin shan rantsuwar shugaban kasa da mataimakinsa.
Teema tayi rubutun ne a shafinta na Instagram inda ta cigaba da cewa, "Ga wani sabon salon shima idan zaki yi, banda waka, tunda kome nayi sai kinyi, kina tare da bakar wahala indai ni zaki dinga kwaikwaya."
Tauraruwar ta saka hoton fastar siyasa da tayi wa Sanatan a shafinta na Instagram a lokacin da tayi wadancan habaicin.
An ga Fati Mohammed ta yiwa Sanata Dino Melaye waka da kumaa fasta ta siyasa.
SOURCE LEGIT.NG
Hotuna : Shugaba buhari yayin sallar jumu'a Yau A Saudiyya. https://t.co/mqVp8dYqhK https://t.co/mqVp8dYqhK May 31, 2019 at 05:07PM
— AREWASOUND (@Arewasound) May 31, 2019

Kannywood: An Nemi Fansar Miliyan 10 Bayan Sace Mataimakin Shugaban MOPPAN
Lamarin sace mutane da yin garkuwa da su ya shigo masana’antar shirin fim din Hausa ta Kannywood, inda a jiya Laraba a ka sace shugaban hadaddiyar kungiyar ‘yan fim fa kasa, Malam Salisu Muazu a kan hanyarsu ta koma wa garin Jos daga Kaduna.
Yayansa Malam Sani Muazu ne ya sanar, inda ya bayyana cewa, “jiya a kan hanyarmu ta komawa Jos daga Kaduna bayan halartar wani taro, mu ka yi kicibis da ‘yan fashi/masu satar mutane a guraren Saya bayan Jengere a yankin karamar hukumar Bassa da ke jihar Filato.
DUNA WANNAN : Kannywood: Kotu ta janye dokar kama wata shahararriyar yar fim din Hausa da ta bayar a baya.
Alhaji Sani, wanda kuma tsohon shugaban MOPPAN ne na kasa, ya kara da cewa, sun samu tuntubar da su a safiyar yau Jumaa, inda a ka nemi a biya diyyar Naira miliyan 10.
Daga nan sai ya roki a sanya su a addu’a tare da fatan Allah ya kawo karshen matsalar tsaron nan a fadin kasar bakidaya.
SOURCE LEADERSHIP. NG
Yayansa Malam Sani Muazu ne ya sanar, inda ya bayyana cewa, “jiya a kan hanyarmu ta komawa Jos daga Kaduna bayan halartar wani taro, mu ka yi kicibis da ‘yan fashi/masu satar mutane a guraren Saya bayan Jengere a yankin karamar hukumar Bassa da ke jihar Filato.
DUNA WANNAN : Kannywood: Kotu ta janye dokar kama wata shahararriyar yar fim din Hausa da ta bayar a baya.
“Sun yi ma na fashi, amma na yi sa’a na tsira, sai dai kuma kanina, Salisu Muazu da wasu abokai guda biyu da mu ka rage wa hanya zuwa Jos a kan hanyarsu ta zuwa Bauchi, Danlami Yanke-yanke da Bature, wadannan Fulanin maharan su sun sace su.”
Alhaji Sani, wanda kuma tsohon shugaban MOPPAN ne na kasa, ya kara da cewa, sun samu tuntubar da su a safiyar yau Jumaa, inda a ka nemi a biya diyyar Naira miliyan 10.
“Sun tuntube mu a safiyar nan, su na masu neman a biya diyyar Naira miliyan 10, in ji shi.
Daga nan sai ya roki a sanya su a addu’a tare da fatan Allah ya kawo karshen matsalar tsaron nan a fadin kasar bakidaya.
SOURCE LEADERSHIP. NG
Wednesday

Kannywood: Kotu ta janye dokar kama wata shahararriyar yar fim din Hausa da ta bayar a baya
Gabon ta karyata cewa ta roki jarumi Nabaraska.
Kotun majistare wacce ke garin Kano ta janye dokar da ta bayar ga kwamishinan ‘yan sanda na ya kamo Hadiza Aliyu Gabon.
Idan bamu manta ba Mustapha Badamasi wanda aka fi sani da Nabraska shine yayi karar jarumar akan zargin taci zarafinsa.
KU KARANTA: Kwana Casa'in - Kashi Na bakwai 7- AREWA24.
Bayan Nabraska ya shigar da karar jarumar zuwa kotun majistare dake Kano, sai kotun ta aikawa Hadiza da sammaci yayin da taki bayyana a gaban kotun.
Shugaban wannan kotun, Muntari Dandago shine ya baiwa kwamishina Muhammad Wakili umarnin a kamo masa wannan jaruma saboda taki amsa gayyatar kotu.
A wani labari mai kama da wannan, Hadiza Aliyu Gabon ta karyata labarin da ake yadawa a kanta na cewa wai 'yan sanda sun kamata sannan kuma ta durkasa har kasa domin neman afuwar Nabraska.
![]() |
| Image© bbc |
Kotun majistare wacce ke garin Kano ta janye dokar da ta bayar ga kwamishinan ‘yan sanda na ya kamo Hadiza Aliyu Gabon.
Idan bamu manta ba Mustapha Badamasi wanda aka fi sani da Nabraska shine yayi karar jarumar akan zargin taci zarafinsa.
KU KARANTA: Kwana Casa'in - Kashi Na bakwai 7- AREWA24.
Bayan Nabraska ya shigar da karar jarumar zuwa kotun majistare dake Kano, sai kotun ta aikawa Hadiza da sammaci yayin da taki bayyana a gaban kotun.
Shugaban wannan kotun, Muntari Dandago shine ya baiwa kwamishina Muhammad Wakili umarnin a kamo masa wannan jaruma saboda taki amsa gayyatar kotu.
A wani labari mai kama da wannan, Hadiza Aliyu Gabon ta karyata labarin da ake yadawa a kanta na cewa wai 'yan sanda sun kamata sannan kuma ta durkasa har kasa domin neman afuwar Nabraska.
Jarumar tayi watsi da wannan labari inda take cewa, " Babu dan sandan da ya kama ni, kuma ni da Mustapha mun yi sulhu ne a harabar kotu amma ban durkusa ma kowa ba. Masu yada wannan labari suna kokarin bata min suna ne kawai."
SOURCE LEGIT.NG
Kwana Casa'in - Kashi Na bakwai 7- AREWA24. https://t.co/Nos04aQAVu https://t.co/Nos04aQAVu May 21, 2019 at 09:19PM— AREWASOUND (@Arewasound) May 21, 2019
Friday

Dandalin Kannywood: Dalilin da ya sa nake auri-saki | Adam Zango
Jarumin ya bayyana cewa ba wai baya iya zama da mace bane, sai dai "ba zan iya fada muku abin da ya hada shi da matata ta farko, da matata ta biyu da kuma matata ta uku ba."
“Allah yana hada mata, mace da namiji. Allah ya halicci mata domin su kasance ni’ima a garemu maza. Don mu Allah ya halicce su."
KU KARANTA KUMA: Abinda yasa Ganduje bai tsige sarki Sanusi II ba - Majiyar gwamnatin Kano.
Adam ya kuma bayyana cewa Allah ya rigada ya tsara ma mutum kaddararsa da abunda zai faru da shi tun kan a haifasa har izuwa ranar da zai amsa kiran mahallicinsa.
SOURCE | LEGIT.NG
“Allah yana hada mata, mace da namiji. Allah ya halicci mata domin su kasance ni’ima a garemu maza. Don mu Allah ya halicce su."
KU KARANTA KUMA: Abinda yasa Ganduje bai tsige sarki Sanusi II ba - Majiyar gwamnatin Kano.
Adam ya kuma bayyana cewa Allah ya rigada ya tsara ma mutum kaddararsa da abunda zai faru da shi tun kan a haifasa har izuwa ranar da zai amsa kiran mahallicinsa.
— AREWASOUND (@Arewasound) May 16, 2019
Dan wasan ya bayyana hakan ne a hira da yayi da shafin BBC Hausa inda yake cewa: "Allah Ubangiji ya rubuta wa mutum abin da zai faru da shi tun daga farkon haihuwarsa har zuwa ranar mutuwarsa."
“Kuma wannan kaddarar da Allah yayi mun itace tawa, saboda ni , Allah yana gani, Allah ya ba ni komai da na roke shi, amma ban da mace wanda nake zaman aure da su.
“Sannan kuma ina so na gayawa mutane wani abu cewa, duk mutin da ya kasance zai yi aure ya rabu da mace, ya kara yi kuma ya kara rabuwa da ita, toh ya kamata su gane cewa wannan mutumin ba mazinaci ba ne. Saboda ni Adamu Zango Allah ya ba ni, duk duniya a cikin masana’antar Kannywood, babu wanda mata ke so iri na. Toh me zan yi da aure?”
SOURCE | LEGIT.NG
Sunday

Kannywood : Hotunan Adam A. Zango da sabuwar amaryar sa
Zango ya angonce da wata mai suna Safiya Umar Chalawa, wacce aka fi kira da Suffy, a ranar juma'a, 26 ga watan Afrilu, da misalin karfe 2:30 na rana.
An daura auren ne a masallacin fadar sarkin Gwandu da ke garin Gwandu, a jihar Kebbi.
Majiyar mu ta sanar da mu cewar Zango ya yi aure sau biyar a baya, ya samu 'ya'ya shida; hudu maza, biyu mata, daga mata biyar da ya aura kafin su rabu.
Sabuwar amaryar Zango
Adam A. Zango da sabuwar amaryar sa
Adam A. Zango da amaryar sa
DUBA WANNAN: Dandalin Kannywood: Dalilan da suka sa zan kai Hadiza Gabon kara kotu - Amina Amal
Amina ce matar Zango ta farko da ya aura a shekarar 2006. Ita ce uwar yaron sa na farko, Haidar, wanda yanzu haka ya cika shekara 12 da haihuwa. Majiyar mu ta ce ba ta san abinda ya raba auren Zango da Amina ba.
Zango ya kara auren wata matar mai suna A'isha, 'yar asalin Shika ta karamar hukumar Zaria a jihar Kaduna. Ta haifa masa 'ya'ya maza uku.
Jarumin ya auri matar sa ta uku mai suna Maryam daga jihar Nasarawa.
Daga bisani ya auri wata jarumar fim mai suna Maryam AB Yola a Lugbe, Abuja a shekarar 2013. Sun bayyana tare a cikin wani shirin fim din Hausa mai suna 'Nas'.
DUBA WANNAN: Mutane 5 Masu HAtsari a Duniya Da Ake Nemansu Ruwa a Jallo
A shekarar 2015, Zango ya auri Ummul Kulsum daga Ngaoundere a jamhuriyar Kamaru. An yi auren a sirrance. Ummul Kulsum ce ta fara haifa wa Zango diya mace, wacce ya sanya wa suna Murjanatu.
Safiyya ko kuma Suffy kamar yadda ake kiranta, ita ce za ta kasance matar Zango ta shida da ya aura.
Majiyar mu ta ce Zango ya saki dukkan mata biyar da ya aura a baya, sai dai har yanzu ba ta san dalilin rabuwar sa da matan da ya ke aura ba.
An daura auren ne a masallacin fadar sarkin Gwandu da ke garin Gwandu, a jihar Kebbi.
Majiyar mu ta sanar da mu cewar Zango ya yi aure sau biyar a baya, ya samu 'ya'ya shida; hudu maza, biyu mata, daga mata biyar da ya aura kafin su rabu.
Sabuwar amaryar Zango
Adam A. Zango da sabuwar amaryar sa
Adam A. Zango da amaryar sa
DUBA WANNAN: Dandalin Kannywood: Dalilan da suka sa zan kai Hadiza Gabon kara kotu - Amina Amal
Amina ce matar Zango ta farko da ya aura a shekarar 2006. Ita ce uwar yaron sa na farko, Haidar, wanda yanzu haka ya cika shekara 12 da haihuwa. Majiyar mu ta ce ba ta san abinda ya raba auren Zango da Amina ba.
Zango ya kara auren wata matar mai suna A'isha, 'yar asalin Shika ta karamar hukumar Zaria a jihar Kaduna. Ta haifa masa 'ya'ya maza uku.
Jarumin ya auri matar sa ta uku mai suna Maryam daga jihar Nasarawa.
Daga bisani ya auri wata jarumar fim mai suna Maryam AB Yola a Lugbe, Abuja a shekarar 2013. Sun bayyana tare a cikin wani shirin fim din Hausa mai suna 'Nas'.
DUBA WANNAN: Mutane 5 Masu HAtsari a Duniya Da Ake Nemansu Ruwa a Jallo
Safiyya ko kuma Suffy kamar yadda ake kiranta, ita ce za ta kasance matar Zango ta shida da ya aura.
Majiyar mu ta ce Zango ya saki dukkan mata biyar da ya aura a baya, sai dai har yanzu ba ta san dalilin rabuwar sa da matan da ya ke aura ba.
Saturday

Dandalin Kannywood: Dalilan da suka sa zan kai Hadiza Gabon kara kotu - Amina Amal
Amal ta bayyana hakan ne ga manema labarai a wata hira da ta yi da su a cikin makonnan, ta yi maganar ne akan bidiyon da ya ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani da ya ke nuna lokacin da Hadiza Gabon ta ke dukan ta.
"Na hadu da wasu lauyoyi kuma sun amince akan za su tsaya mini don kwato mini hakkina," in ji ta.
"Addu'ar da nake ita ce Allah ya sa na samu damar dawo da darajata a idon al'umma. Da irin abinda ya faru, yanzu na san mutane da yawa suna yi mini wani irin kallo, duk da cewa duk abinda ya faru dama an gama shirya shi ne domin a bata mini suna a idon duniya. A cikin bidiyon, za ku ga yadda ta ke dukana tana ci mini zarafi, fatan da nake Allah ya taimakeni na wanke bata sunan da aka yi mini."
Yayin da take bayani game da abin da ya faru tsakaninta da Hadiza Gabon, Amal ta ce: "Abin da ya faru shi ne, na sanya wani rubutu a daya daga cikin kafafen sadarwa, ban san cewa abinda na rubuta din zai batawa Hadiza Gabon rai ba, wacce ni ina daukarta a matsayin abar koyi a gurina.
"Da farko hotone na saka wanda bai dace ba, hakan ya jawo mutane da yawa suka yi ta faman magana akan hoton, sai daga baya na dan yi rubutu akan hoton.
KU KARANTA: Duba : Jerin Jihohin Nigeria Da Akafi Fama Da Rashin Aikin Yi.
"Ni ban san cewa rubutun na wa ya bata mata rai ba, saboda ban kira sunan kowa a cikin rubutun nawa ba. A wannan ranar ina zaune a gida sai Habu Sarki, wanda yana daya daga cikin mutanen da nake ganin mutuncinsu sosai a masana'antar mu, ya kirani ya ce yana so muyi wata magana mai muhimmanci.
"Ya ce yanzu baya gari amma idan ya dawo zai kirani. Ya na dawowa ya kirani kamar yadda muka yi dashi, ina fitowa daga gida sai naga Hadiza Gabon ta na fitowa daga mota.
"Ban san cewa ta zo tare da wasu ba a cikin Keke Napep, ta na zuwa kusa dani ta rufe ni da duka. Sai Habu Sarki ya ce mu shiga cikin gida, sai gaba daya kaina ya daure saboda ban san menene ke faruwa ba. Sai na bude gida muka shiga dukan mu, amma har lokacin ba ta dai na dukana ba. Idan kun kalli bidiyon da kyau zaku ga cewa abun ya faru a cikin gidane. Bidiyon guda biyu ne, ta dake ni sosai sannan ta kwace wayata."
KU KARANTA: Manyan likitoci Biyar sun shigo Nigeria don Duba lafiyar Zakzaky.
Ta ce Hadiza Gabon, da direban ta da wasu mutane, sun sake dukanta kwana daya bayan wancan abun ya faru, lokacin da ta je shagonta domin ta roketa akan ta bata wayarta da ta kwace a wurinta.
Ta nuna wa manema labaran ciwon da Hadiza Gabon din ta ji mata a fuskarta, domin su tabbatar da cewa ta dake ta.
"Na hadu da wasu lauyoyi kuma sun amince akan za su tsaya mini don kwato mini hakkina," in ji ta.
"Addu'ar da nake ita ce Allah ya sa na samu damar dawo da darajata a idon al'umma. Da irin abinda ya faru, yanzu na san mutane da yawa suna yi mini wani irin kallo, duk da cewa duk abinda ya faru dama an gama shirya shi ne domin a bata mini suna a idon duniya. A cikin bidiyon, za ku ga yadda ta ke dukana tana ci mini zarafi, fatan da nake Allah ya taimakeni na wanke bata sunan da aka yi mini."
Yayin da take bayani game da abin da ya faru tsakaninta da Hadiza Gabon, Amal ta ce: "Abin da ya faru shi ne, na sanya wani rubutu a daya daga cikin kafafen sadarwa, ban san cewa abinda na rubuta din zai batawa Hadiza Gabon rai ba, wacce ni ina daukarta a matsayin abar koyi a gurina.
"Da farko hotone na saka wanda bai dace ba, hakan ya jawo mutane da yawa suka yi ta faman magana akan hoton, sai daga baya na dan yi rubutu akan hoton.
KU KARANTA: Duba : Jerin Jihohin Nigeria Da Akafi Fama Da Rashin Aikin Yi.
"Ni ban san cewa rubutun na wa ya bata mata rai ba, saboda ban kira sunan kowa a cikin rubutun nawa ba. A wannan ranar ina zaune a gida sai Habu Sarki, wanda yana daya daga cikin mutanen da nake ganin mutuncinsu sosai a masana'antar mu, ya kirani ya ce yana so muyi wata magana mai muhimmanci.
"Ya ce yanzu baya gari amma idan ya dawo zai kirani. Ya na dawowa ya kirani kamar yadda muka yi dashi, ina fitowa daga gida sai naga Hadiza Gabon ta na fitowa daga mota.
"Ban san cewa ta zo tare da wasu ba a cikin Keke Napep, ta na zuwa kusa dani ta rufe ni da duka. Sai Habu Sarki ya ce mu shiga cikin gida, sai gaba daya kaina ya daure saboda ban san menene ke faruwa ba. Sai na bude gida muka shiga dukan mu, amma har lokacin ba ta dai na dukana ba. Idan kun kalli bidiyon da kyau zaku ga cewa abun ya faru a cikin gidane. Bidiyon guda biyu ne, ta dake ni sosai sannan ta kwace wayata."
KU KARANTA: Manyan likitoci Biyar sun shigo Nigeria don Duba lafiyar Zakzaky.
Ta ce Hadiza Gabon, da direban ta da wasu mutane, sun sake dukanta kwana daya bayan wancan abun ya faru, lokacin da ta je shagonta domin ta roketa akan ta bata wayarta da ta kwace a wurinta.
Ta nuna wa manema labaran ciwon da Hadiza Gabon din ta ji mata a fuskarta, domin su tabbatar da cewa ta dake ta.
Subscribe to:
Posts (Atom)



