Thursday

Home Nafisat Abdullahi ta sanar da komawar ta Kamfanin Kannywood.
Yar wasar fin din Hausa Nafisat Abdullahi ta
sanar da komawar ta kamfanin Kannywood
bayan wani dogon hutu.




Nafisat ta amshi lambar yabo a mastayin jarumar
Kannywood da ta fi iya wasa a shekarar
2015/2016 sannan kuma ta karbi lambar yabo na
kannywood a shekarar 2016/2017.

KU KARANTA KUMA: Mugun nufi: Yadda aka
nemi a kashe shugaba Buhari


Kusan kimanin shekara daya kenen da jarumar
mai shekaru 25 ta dakatar da fitowa a wasannin
Kannywood. Ta sanar da dawowar ta ne a shafin
ta na Instagram.
An yarda da cewan ta mayar da hankalin ta ne a
sabon gidauniyar ta “The Love Laugh
Foundation” wanda ta kaddamar kwanan nan a
Kaduna.

An taba dakatar da Nafisat daga Kannywood a
shekarar 2013 sakamakon wani liyafa da ta
shirya sannan ta ki gurfana a kaban kwamitin
ladabtarwa.
No comments:
Write Comments