Showing posts with label hotuna. Show all posts
Showing posts with label hotuna. Show all posts

Friday

Hotuna : Shugaba buhari yayin sallar jumu'a Yau A Saudiyya.

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi sallar Juma'a a babban masallacin Makkah da ke Saudiyya tare da kimanin shugabanin kasashen duniya 53 da daruruwan mabiya addinin musulunci.

Kamfanin dillancin labarai NAN ta ruwaito cewa Buhari da sauran shugabanin kasahen duniya sun tafi kasa mai tsarkin ne domin hallartar taron Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi (OIC) karo na 14.

Taron wadda Sarkin Saudiyya Salman bin Abdulaziz Al Saud ne mai masaukin baki zai fara ne misalin karfe 12 na dare.

Wadanda suka yiwa shugaba Buhari rakiya sun hada da gwamnonin jihar Osun, Niger da JIgawa.

An sa ran shugaba Buhari zai gana da wasu shugabani kasashen duniya kafin ya dawo gida Najeriya a ranar Lahadi kamar yadda NAN ta ruwaito.


Shugaba Buhari da shugaban NITDA, Aliyu Pantami da Shugaba Macky Sall na Senegal a Makkah


Shugaba Buhari tare da takwararsa na kasar Chadi, Idris Deby bayan sallar Juma'a a Makkah


Shugaba Buhari tare da shugaban kasar Chadi, Idris Deby bayan sallar Juma'a a masallacin Makkah

DUBA WANNAN: Diyar Atiku ta ce ba za ta taba mantawa da mulkin APC ba


Shugaba Buhari da Shugaba Idris Deby na Chadi da Macky Sall na Senegal bayan sallar Juma'a a Makkah

SOURCE LEGIT.NG

Thursday

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya sauka a birnin Madina : Hotuna

Mun samu cewa a Yammacin yau Alhamis, 16 ga watan Mayun 2019.

shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa birnin Madina na kasar Saudiya domin gudanar da ibadar Umarah a cikin wannan babban wata na Azumin Ramalana.

DUBA WANNAN : Kwana Casa'in - Kashi Na Shida 6 - AREWA24.  

Buhari in makka

Ziyarar shugaban kasa Buhari ta yi daidai da amsa goron gayyata na masarautar Saudiya karkashin jagorancin Sarki Salman Bin Abdulaziz kamar yadda fadar shugaban kasa ta bayyana.






Saturday

Bidiyo : Gwamnan Kano Dr, Abdullahi Umar Ganduje Yayin Tabbatar da Nadin sarakunan Yanka.

Mai Girma Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje OFR da Mataimakin sa Dr Nasiru Yusuf Gawuna sum iiso dakin taro na Sani Abacha Stadium domin bikin karbar takardun sababbin Sarakunan Rano, Bichi, Karaye da Gaya wanda aka basu jiya Jumu'a.

ganduje
Sarakunan hudu da aka yiwa nadin sun hada da; Sarkin Rano Alhaji Tafida Abubakar Ila, Sarkin Gaya Alhaj Ibrahim Abdulqadir Gaya, Sarkin Bichi Alhaji Aminu Ado Bayero, Sarkin Karaye Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II.

KARANTA WANNAN : Dalilan da yasa kotu ta yi gaggawar dakatar da Ganduje   

Yayin bikin nadin sarautan, Gwamna Ganduje ya ce sabbin masarautun da aka kirkira za su inganta masarautar Kano.
"Mun san cewa wannan sabbin masarautun za su inganta tsaro da ilimi," a cewar Ganduje.

Gwamnan ya kuma ce gwamnati za ta sanar da ranakun da za a yiwa sarakunan bikin nadi na musamman a nan gaba.

alumma

A baya dai kunji cewar kotu a kano ta dakatar da  gwamnati kan batun nadin sabbin sarakunan, sai dai lokacin da labarin dakatar da gwamnatin jihar Kano da kotu tayi daga kafa sabbin masarautu a jihar Kano, kwamishinan shari’ah na jihar, Barista Ibrahim Mukhtari ya bayyana cewa har zuwa daren ranar Juma’a, 10 ga watan Mayu, bai amshi wani umurni daga kotu akan lamarin nadin sabbin saranan ba.



READ HERE: Top 5 animal that has the longest life span.  



The vedio from Arewasound-channel.

 Da farko dai an rawaito cewa wata babbar kotun jihar Kano, ta dakatar da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje daga kafa sabbin masarautu hudu da majalisar dokokin jihar ta yi.


Monday

Yanzu-Yanzu : Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Dahiru Dahiru Bauchi (Hotuna)

A ranar Asabar, 27 ga watan Afrilu, dan takarar gwamnan jihar Kano a karkashin inuwar jam'iyyar PDP a zaben da aka kammala, Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida), ya kai wa babban shehun darikar Tijjaniya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ziyara a gidansa dake Kano.
Abba kabar yusuf, abba gida gida, abba gida gida song, wakar abba gida gida

Dan takarar ya samu rakiyar dan takarar mataimakinsa, Kwamred Aminu Abdulsalam, tare da wasu magoya baya da masoyan sa.

Abba Gida-Gida ya ziyarci Dahiru Dahiru Bauchi
Abba kabar yusuf, abba gida gida, abba gida gida song, wakar abba gida gida


Abba Gida-Gida a gidan Dahiru Dahiru Bauchi

Jam’iyyar tana nema kotu ta soke nasarar da gwamna mai-ci Dr. Abdullahi Umar Ganduje na jam’iyyar APC mai mulki ya samu a zaben na bana.

DUBA WANNAN: Kannywood : Hotunan Adam A. Zango da sabuwar amaryar sa 

PDP tana so ne a ba ‘dan takararta, Injiniya Abba K. Yusuf nasara a zaben na 2019. Lauyoyin PDP sun fadawa kotun karar zaben cewa ‘dan takarar ta na 2019, Abba Kabiru Yusuf, ya samu kuri’un da ake nema wajen lashe zaben gwamna don haka ta nemi a bayyana shi a matsayin zababben gwamna na jihar Kano.
Abba kabar yusuf, abba gida gida, abba gida gida song, wakar abba gida gida

Abba Gida-Gida a gidan Dahiru Dahiru Bauchi.
Abba kabar yusuf, abba gida gida, abba gida gida song, wakar abba gida gida

Abba Gida-Gida ya ziyarci Dahiru Bauchi
Abba kabar yusuf, abba gida gida, abba gida gida song, wakar abba gida gida

A karar da PDP ta maka a gaban kotun mai sauraron korafin zabe mai shafi 1685. Jam’iyyar hamayyar tana ja da soke zaben wasu yankuna a cikin karamar hukumar Nasarawa da hukumar zabe mai zaman kan-ta tayi a watan jiya.

Sunday

Kannywood : Hotunan Adam A. Zango da sabuwar amaryar sa

Zango ya angonce da wata mai suna Safiya Umar Chalawa, wacce aka fi kira da Suffy, a ranar juma'a, 26 ga watan Afrilu, da misalin karfe 2:30 na rana.
Adam a zango da amaryarsa,  amaryar adam a zango

An daura auren ne a masallacin fadar sarkin Gwandu da ke garin Gwandu, a jihar Kebbi.

Majiyar mu ta sanar da mu cewar Zango ya yi aure sau biyar a baya, ya samu 'ya'ya shida; hudu maza, biyu mata, daga mata biyar da ya aura kafin su rabu.
Adam a zango da amaryarsa,  amaryar adam a zango

Sabuwar amaryar Zango
Adam A. Zango da sabuwar amaryar sa
Adam A. Zango da amaryar sa

DUBA WANNAN: Dandalin Kannywood: Dalilan da suka sa zan kai Hadiza Gabon kara kotu - Amina Amal

Amina ce matar Zango ta farko da ya aura a shekarar 2006. Ita ce uwar yaron sa na farko, Haidar, wanda yanzu haka ya cika shekara 12 da haihuwa. Majiyar mu ta ce ba ta san abinda ya raba auren Zango da Amina ba.

Zango ya kara auren wata matar mai suna A'isha, 'yar asalin Shika ta karamar hukumar Zaria a jihar Kaduna. Ta haifa masa 'ya'ya maza uku.
Adam a zango da amaryarsa,  amaryar adam a zango

Jarumin ya auri matar sa ta uku mai suna Maryam daga jihar Nasarawa.

Daga bisani ya auri wata jarumar fim mai suna Maryam AB Yola a Lugbe, Abuja a shekarar 2013. Sun bayyana tare a cikin wani shirin fim din Hausa mai suna 'Nas'.

DUBA WANNAN: Mutane 5 Masu HAtsari a Duniya Da Ake Nemansu Ruwa a Jallo  

A shekarar 2015, Zango ya auri Ummul Kulsum daga Ngaoundere a jamhuriyar Kamaru. An yi auren a sirrance. Ummul Kulsum ce ta fara haifa wa Zango diya mace, wacce ya sanya wa suna Murjanatu.

Safiyya ko kuma Suffy kamar yadda ake kiranta, ita ce za ta kasance matar Zango ta shida da ya aura.
Majiyar mu ta ce Zango ya saki dukkan mata biyar da ya aura a baya, sai dai har yanzu ba ta san dalilin rabuwar sa da matan da ya ke aura ba.

Monday

Hotuna : Shugaban Sojin sama ya nishadantar da Sojoji dake yaki da Boko Haram

Babban hafsan rundunar mayakan Sojan sama, Air Marshal Saddique Abubakar ya shirya ma zaratan dakarun Sojin saman Najeriya dake fafatawa a filin daga na jahar Borno, liyafar cin abinci tare da nishadantar dasu.

Sadiqque ya shirya wannan liyafar ce a ranar Litinin, 22 ga watan Afrilu a garin Maidugurin jahar Borno, inda aka ci abinci mai rai da lafiya tare da nama iya nama, aka kuma sha kayan shaye shaye da tande tande, sa’annan aka nishadantu da dadadan wakokin bare bari.

KU KARANTA: Kwana Casa'in Kashi Na 3 : AREWA24 Channel.   

Legit.ng ta ruwaito kaakakin rundunar Sojan sama, Ibikunle Daramola ne ya bayyana haka a ranar Litinin, inda yace Saddique na amfani da damar irin wannan liyafa don ganawa da dakarun Sojinsa a duk lokacin da ake wani sha’anin biki, don haka ya shirya musu wannan saboda bikin Easter da kiristoci ke yi.

Kaakakin ya kara da cewa Saddique na amfani da wannan dama don gode ma Sojojinsa, tare da jinjina musu bisa kokarin da suke yi wajen yaki da ta’addanci a yankin Arewa maso gabas, sa’annan yace irin wanna taro na dauke ma Sojojin kewar rashin iyalansu a kusa.

Babban hafsan Sojan sama ya nishadantar da Sojojin dake yaki da Boko Haram
Haka zalika baya ga Sojojin da suka halarci liyafar, rundunar ta gayyaci al’umma unguwar Gomari, unguwar da sansanon rundunar Sojan sama take zuwa wannan liyafa, inda kuma dayawansu suka amsa kira, suka ci, suka sha, suka yi nak!.

Daga karshe kaakaki Daramola yace rundunar ta gudanar da irin wannan liyafar cin abinci a sansaninta dake Yola, da kuma sansaninta dake jahar Katsina.

SOURCE LEGIT.NG