Showing posts with label ta'addanci. Show all posts
Showing posts with label ta'addanci. Show all posts

Monday

Yanzu-yanzu: Yan bindiga sun budewa sabon gwamnan Zamfara wuta

A jiya Lahadi ne, wasu yan bindiga sun budewa motar sabon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, wuta yayinda yake hanyarsa na jajintawa wadanda suka rasa yan uwansu a wani hari da aka kai karamar hukumar Gusau, Premium Times ta bada rahoto.

Masu Idanuwan shaida sun bayyana cewa an budewa motar gwamnan wuta ne da yammacin Lahadi a hanyar garin Lilo.

Majiya ya bayyana cewa Yayinda suka kai harin, yan bindigan sun yi amfani da damar tsayin ciyayi inda suka bude masa wuta.

Ya kara da cewa zuwa yanzu ba'a san yawan wadanda aka rasa ko suka jikkata ba, saboda masu tsaron gwamnan sun yi batakashi da yan bindigan.

KU KARANTA: Yadda Wani dalibi ya kashe kansa a dalilin sabani da budurwarsa.

A rahoton da muka kawo da saifyar yau, mai magana da yawun Sabon gwamnan jahar Zamfara, Bello Matawalle ya bayyaa cewa gwamnan ya jagoranci ayarin jami’an rundunonin tsaro inda suka fantsama cikin dazukan kauyen Wonaka dake garin Gusau da nufin farautar miyagun yan bindiga da suka addabi al’ummar yankin.

Kaakakin, Yusuf Idris ya bayyana haka cikin wata sanarwa daya fitar a ranar Lahadi, 2 ga watan Yuni, inda yace gwamnan ya samu rakiyar mataimakin gwamnan jahar, Mahadi Aliyu Gusau, da sauran kwamandojin rundunar tsaro, inda suka fatattaki yan bindigan.

A ranar Asabar, Akalla mutane 8 sun rasa rayukansu yayinda 18 suka jikkata harin da aka kai garin Lilo.

Har ilayau, jihar Zamfara da wasu jihohi basu gushe suna fuskantar barazana daga wajen yan bindiga ba.

SOURCE LEGIT.NG


Buhari ya bada umarnin sakin mutanen Nigeria uku da saudiyya ta kama.

Ciki Harda Daliba Zainab Daga Kano.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci ministan shari'a, Abubakar Malami, da ya tabbatar da cewar hukumomin kasar Saudiyya sun saki matashiyar nan yar Najeriya, Zainab Aliyu, da aka yi kuskuren kama wa bisa zargin laifin safarar kwaya.

Hukumomin kasar Saudiyya sun kama Zainab, daliba a jami'ar Maitama Sule dake Kano, a ranar 26 ga watan Disamba na shekarar 2018 bisa zarginta da shiga da jaka dauke da kwayar 'tramol' zuwa kasar Saudiyya.
Zainab Aliyu
Daliba Zainab Aliyu

Matashiyar ta tashi zuwa kasar Sauddiya daga filin jirgin sama na Mallam Aminu domin gudanar da aikin 'umra' tare da mahaifiyarta, Maryam, da 'yar uwarta, Hajara.

Babbar mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren harkokin da suka shafi kasashen waje, Abike Dabiri Erewa, ce ta sanar da umarni da shugaba Buhari ya bayar a ranar Litinin, 29 ga watan Afrilu, ta kara da cewa tuni gwamnatin tarayya ta fara tattauna batun sakin Zainab tare da wasu mutane biyu dake da irin matsalar da Zainab ta samu.

" Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci ministan shari'a ya dauki matakan da suka dace a kan matsalar matashiyar. Mun fara tattauna wa da hukumomin kasa, za ta dawo gida tare da wasu mutane biyu dake da irin wannan matsala," kamar yadda Dabiri ta sanar a shafinta na Tuwita.

DUBA WANNAN: Mutane 5 Masu HAtsari a Duniya Da Ake Nemansu Ruwa a Jallo. 

Mahaifin Zainab ne ya fara rubuta wata takardar korafi da ya aika wa hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) a kan zargin cewar an saka kwaya a jakar diyar sa.

Daga bisani, binciken NDLEA ya gano cewar akwai gungun wasu ma'aikan kamfanonin jirgin sama da suka kware wajen yin cushen kwayoyi a jakankunan matafiya.

Thursday

Soyayya batayi rana ba : Rikicin masoya ya Aika wani saurayi har lahira.

Wani matashi dan shekara 29 dake aikin tuka kwale-kwale a jahar Bayelsa, Alabo Enai ya hallaka kansa sakamakon bakin ciki daya turnukeshi bayan samun wani dan sabani tsakaninsa da budurwarsa Blessing.
Rikicin masoya, nishadin masoya

Majiyarmu ta ruwaito matashi Alabo dan haifaffen karamar hukumar Brass a jahar Bayelsa sun samu matsala ne da budurwarsa Blessing yar kabilar Ologbobiri a karamar hukumar Ijaw ta kudu, wanda hakan ta kai ga alakarsu tana tangal-tangal.

KU KARANTA: Radadin Talauci : Wani mutum ya bankawa kansa wuta...   

Duk kokarin da matashin saurayin yayi na shawo kan budurwarsa yaci tura, wanda hakan yayi sanadiyyar kashe kansa inda yayi amfani da ragar kama kifi ya daure wuyarsa daga saman bishiya, ma'ana dai ya rataye kansa, abin mamaki kuma wannan budurwa Blessing ce ta gano gawarsa a rataye.

Wani ganau ya bayyana cewa "Cikin kankanin lokaci jama"a suka taru suna kallon gawar matashin, sun mamakin dalilin da yasa ya hallaka kansa, ga shi kuma bai bar wani sako ko wata wasika ba, badurwar ta bayyana cewa sun samu matsala da saurayin nata watakila hakan ne yasa ya aikita wannan danyen hukunci.

Ita ma budurwa tayi karin haske kamar haka “Matsalar da ta faru tsakanin mu itace na fada masa ina son zan koma garinmu a kudancin Ijaw, shi kuma ya nuna bai amince da hakan ba, amma da na fahimci ranshi ya baci sai na hakura muka cigaba da zama tare, a wannan ranar daya mutu sai da nace masa yazo mu tafi wasan Easter, amma sai yaki, yace na tafi kawai.”

MAJIYA LEGIT.NG

Tuesday

Radadin Talauci : Wani mutum ya bankawa kansa wuta...

An garzaya da Nweze zuwa asibitin koyar wa na jami'ar Alex Ekwueme da ke Abakaliki domin ceto rayuwar sa bayan ya banka wa kansa wuta a bayan ajin makarantar firamare ta St. Patrik da ke unguwar Kpirikpiri, a Abakaliki, babban birnin jihar Ebonyi.

Talauci, ya kona kansa

Rahotanni sun bayyana cewar Nweze ya daure kafafunsa kafin ya cinna wa kansa wuta.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Ebonyi, Lovett Odah, ya ce suna binciken lamarin domin tabbatar da gaskiyar cewar kashe kansa ya yi.

Ana saura kwana daya ya aikata hakan, Nweze, dan asalin garin Umuogharu a karamar hukumar Ezza ta Arewa, ya yiwa makobtansa korafin cewar ya gaji da rayuwar fatara da rashi da suka sa ko ciyar da kansa ba ya iya yi.

DUBA WANNAN: Yadda ake mayar da hakora suyi haske Æ™al-Æ™al a cikin awa daya  

A cewar kakakin rundunar 'yan sandan; " mun gaggauta aika motar daukan masu bukatar taimakon gagga wa zuwa wurin da abin ya faru bayan mun samu kira daga wani mutum.

" Yanzu haka muna kan gudanar da bincike a kan lamarin, ba mu samu isassun bayanan da zasu tabbatar mana da cewar kashe kansa ya yi ba, ko kuma wani abu ne daban ya faru ba ."

MAJIYA : LEGIT. NG

Friday

Zalunci: Shugaban Makaranta ya kone wata 'Daliba kurmus bayan ta tona masa asiri

Mutuwar wannan budurwa mai shekaru 19 kacal a duniya, Nusrat Jahan Rafi, ya haifar da mummunar zanga-zanga a yankin kasar dake nahiyyar Kudancin Asia. Firai Ministan kasar, Sheikh Hasina ya sha alwashin hukunta dukkanin masu hannu cikin wannan zalunci.
tearcher burned his student in Bangladesh
Bayan da masu hannu cikin wannan muguwar aika-aika sun gaza samun biyan bukata yayin da suka nemi Nusrat ta janye korafin keta mata haddi, sun yi mata wanka da makamashi na Kalanzir kuma suka kone kurmus.


Hukumar 'yan sanda yayin karin haske dangane da wannan lamari na takaici ta bayyana cewa, ta samu nasarar cafke mutane 17 ababen zargi inda daya daga cikin su ya amsa laifi sa da cewa sun aikata hakan ne bisa umurni na shugaban makaranta.

Babban jami'in dan sanda mai gudanar da bincike a kan wannan mugun ji da mugun gani, Muhammad Iqbal, ya shaidawa manema labarai na jaridar AFP cewa, Nusrat ta riga mu gidan gaskiya a ranar 10 ga watan Afrilu inda ba ta gushe ba wajen ci gaba da bayyana koke a kan shugaban makarantar da ya keta mata haddi.

KARANTA KUMA: Hattara! : "Yan ta'addar jihar zamfara sun fara kaura suna shiga wasu jahohi.

Jagorar kungiyar kare hakkin bil Adama ta kasar, Meenakshi Ganguly, yayin babatu na neman a tabbatar da yiwa Nusrat adalci tare da nema mata hakki, ta kuma bayyana yadda gwamnatin kasar Bangladesh ta gaza ta fuskar kare al'umma daga cin zarafi.

SOURCE LEGIT. NG

Hattara! : "Yan ta'addar jihar zamfara sun fara kaura suna shiga wasu jahohi.

A ranar Alhamis dinnan ne da ta gabata, gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola, ya bukaci jami'an tsaro da sarakunan gargajiya da su lura sannan kuma su dakile duk wani shiri na 'yan ta'addar jihar Zamfara, wadanda suke yin kaura daga jihar suna komawa wasu jihohi.

zamfara killings, kashekashen zamfara

Hakan ya biyo bayan sanarwar da babban sakatarensa a fannin sadarwa ya fitar, Mista Adeniyi Adesina, bayan gwamnan ya yi magana a wurin wani taro, akan gudanar da tsarin tsaro, wanda sarakunan gargajiya, shugabannin hukumomin tsaro, kungiyoyin jama'a, 'yan siyasa, 'yan kasuwa da sauransu suka hallata a Osogbo.


Oyetola ya ce "ya zama wajibi a sanya matakan da za su magance matsalar 'yan ta'adda da ke faruwa a jihar Zamfara shigowa jihar Osun."
Gwamnan ya jaddada bukatar tabbatar da tsaro ta hanyar tattara bayanai, sannan sarakunan gargajiya su saka ido a yankunansu da kuma bukatar a fadakar da jami'an tsaro su sanya ido wurin dakile duk wani shiri na ta'addanci a jihar.

Gwamnan da kuma jami'an tsaro sun gargadi masu bada gidajen haya, akan bai wa mutane wadanda ba su da kyakkyawar masaniya a kansu.

KU KARANTA: A karon farko an yiwa wasu birai dashen kwakwalwar Dan-Adam.
"Idan ka bawa mutumin da baka san shi ba hayar gida, kuma muka gano cewa dan ta'adda ne, to duk abinda ya biyo baya kai ka jawowa kan ka," in ji Oyetola.

Ya bukaci sarakunan gargajiya da su yi aiki tukuru, domin masu hakar ma'adanai suna nan suna yawo a wasu yankuna na cikin jihar.

Gwamnatin tarayya ta hana hakar ma'adanai a jihar Zamfara, bayan ta samu bayanan cewa 'yan ta'addar jihar su na da alaka da masu hakar ma'adanai wadanda ba su da lasisi.

SOURCE LEGIT.NG

Thursday

Jerin mutanen da sojoji suka kashe yayin kai hari akan "yan ta'adda ; Cewar Sarakunan zamfara

A jiya Laraba, 17 ga watan Afrilu, majalisar sarakunan Zamfara sun saki jerin sunayen mutanen garin da harin ya kashe su 11 yayinda aka kaiwa yan bindiga harin a karamar hukumar Zurmi.
zamfara killings

Sunayen sune:

Mai Daji Barau,

Na Dumburum,

Suwaiba Alka,

Yar Guru Na Dumburum,

Maryam Shafiu,

Dahe Malan Sule,

Buhari Dan Kurma,

Zaliha na Dumburum,

Aisha Akilu,

Alamin Alka

Fati ‘Yar Gum.

A cewar sarakunan, wasu mutane 11 sun samu raunuka sakamakon wadannan hare-hare a garin Dumburum, karamar hukumar Zurmi na jihar ranar 9 ga watan Afrilu, 2019.
Sunayen wadanda suka samu raunukan sune:

Haruna Kusu,

Muhammad M Sani,

AbdulRazak Abubakar,

Yakubu Yunusa,

Dan Diyya,

Sa’a Dayyabu,

Yar’wargi Mamman,

Gwamna na Dumburum,

Rashida Alka,

Maryam Akilu

Sadiq Sukuranu.

KARANTA WANNAN : Babu Batun cire tallafin mai a Najeriya - NNPC ta magantu 

Kana sun ambaci cewa akwai mutane 20 da aka harin ya rusawa muhalli.
A hira da manema labarai da suka gabatar a Gusau, Wakilin sarakunan jihar, Sarkin Fulanin Bungudu, Alh Hassan Attahiru ya jaddada cewa hari sojin ya kashe al'ummar gari.

SOURCE LEGTI.NG

Wednesday

Gudun abin kunya: Yadda Tsohon shugaban kasa ya harbe kan sa

Tsohon shugaban kasa Garcia, wanda ke fuskantar tuhumar cin hanci, ya harbe kan sa ne da safiyar ranar Laraba bayan jami'an 'yan sanda sun isa gidansa, kamar yadda kafafen yada labarai a kasar Peru suka sanar.
Alan Garcia kill him self,  Alan Garcia shoot himself

Shugaban kasar Peru, Martin Vizcarra, wanda labarin mutuwar ya matukar girgiza shi, ya rubuta a shafinsa na dandalin sada zumunta (Tuwita) cewar; "ina mika sakon ta'aziyya ta ga iyali da masoyan sa ."

An garzaya da Garcia zuwa asibitin Casimiro Ullola domin ceto rayuwar sa, kamar yadda ministan lafiyaa kasar, Zulema Tomas, ya fada wa manema labarai. Ya ce an kai tsohon shugaban kasar asibiti cikin mawuyacin hali.

Tomas ya ce an kai Garcia asibitin da misalin karfe 6:45 na safe, sannan an shiga da shi dakin tiyata bayan mintuna 15 da kai shi. Ministan ya ce sau uku tsohon shugaban kasar na samun bugun zuciya a lokacin da ake yi masa tiyata.

DUBA WANNAN: Kotu ta bawa EFCC damar kama wasu manyan ministoci biyu a gwamnatin PDP

Garcia, mai shekaru 69, ya kasance shugaban kasa a kasar Peru har sau biyu; daga sheakarar 1985 zuwa 1990 a karo na farko da kuma daga shekarar 2006 zuwa 2011 a karo na biyu. Ya kara tsaya wa takara a shekarar 2016, amma ya gaza samun kaso 6% na kuri'un da aka kada.

'Yan kungiyar asiri 151 sun fada tarkon hukumar 'yan sanda cikin wata jiha a Najeriya -

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa, hukumar 'yan sanda ta samu nasarar cafke 'yan kungiyar asiri 151 a jihar Anambra biyo bayan matsin lamba na sintiri da kai komo da ta dabbaka a tsakanin ranar 1 zuwa 16 ga watan Afrilun 2019.
yan kungiyar asiri

SP Muhammad Haruna, kakakin rundunar 'yan sanda na jihar, shi ne ya bayar da shaidar hakan cikin wata sanarwa yayin ganarwar sa da manema labarai a ranar Talatar da ta gabata cikin birnin Awka.

Babban jami'in 'yan sandan ya ce hukumar ta kuma samu nasarar cafke miyagun makamai da wasu kayan maye da ake zargin ciyawa ce ta tabar wiwi. Kazalika SP Haruna ya ce cikin ababen zargin da aka cafke akwai kimanin Yara 20 da hukuncin doka bai rataya a wuyan su ba.

Yayin bayar da tabbacin ci gaba da bincike a kan miyagun ababe domin gurfanar da su a gaban Kuliya, kakakin 'yan sandan ya nemi hadin kan al'umma wajen shigar da rahoton duk wasu ababe na rashin yarda da ke aukuwa a zamantakewar su.


Cikin wani rahoton da jaridar Legit.ng ta ruwaito, a ranar Lahadin da ta gabata rikicin makiyaya da manoma ya salwantar da rayukan Mutane 16 tare da raunata kimanin Mutane 14 a kauyen Numa da ke karkashin karamar hukumar Akwanga ta jihar Nasarawa.

DUBA WANNAN : 'Dan gani kashenin Kwankwasiyya ya tsira bayan kwashe kwanaki 13 a hannun DSS.  

Sunday

Bayan matsin lamba, Buhari ya yi magana a kan matsalar tsaro a Zamfara

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar da tabbacin cewar gwamnatinsa zata kawo karshen aiyukan ta'addanci a jihar Zamfara tare da bayyana cewar yin hakan na daga cikin abubuwan da ya bawa fifiko.

buhari talk about zamfara

Bayan ya sha fama da matsin lamba a kan ya yi magana a kan tabarbarewar tsaro a jihar Zamfara, s

An samu kiraye-kiraye da zanga-zanga daga 'yan Najeriya dake cikin gida da na kasashen ketare a kan a saka dokar ta baci a jihar Zamfara saboda yadda 'yan bindiga ke kashe mutane a kullum.

A wani jawabi da Garba Shehu, kakakin shugaban kasa ya fitar, Buhari ya ce zai dauki duk wani mataki da zai bawa jami'an tsaron Najeriya damar murkushe duk wasu makiya Najeriya.

Bayan fitar da wannan sanarwa da Garba Shehu ya yi, shi kansa shugaba Buhari ya bayyana cewar bai amince da zargin da wasu ke yi masa a kan cewar bai damu da asarar rayukan da ake yi a jihar Zamfara ba.

Top3

A jerin wasu sakonni da ya fitar a shafinsa na tuwita, shugaban Buhari ya ce; " abin mamaki ne da rashin adalci a ce ban damu da halin da jihar Zamfara ke ciki ba ko kuma bana yin komai a kai. Babban aiki na a matsayin shugaba shine tabbatar da tsaron lafiya da dukiyoyin 'yan Najeriya. Babu wani abu dake raina fiye da yin hakan.

DUBA WANNAN: Kisan kare dangi: 'Yan Zamfara sun gudanar da zanga-zanga a Abuja

"A shirye muke domin ganin mun shawo kan kalubalen tsaro tare da murkushe masu kashe mutane. Mun tura jami'an tsaro zuwa dukkan sassan da ake kai hare-hare, kuma zamu cigaba da sabunta hanyoyi da dabarun yaki da aiyukan 'yan ta'adda.
"Ina tuntubar shugabannin rundunar tsaro domin jin abubuwan dake faruwa a Zamfara da ragowar sassan kasa. Ina bayar da tabbacin cewar zamu cigaba da bawa jami'an tsaro hadin kan da suke bukata domin ganin sun kawar da duk wani kalubalen tsaro da muke fama da shi."

Thursday

Hotuna : Yadda gwamna elrufai ya fatattaki masu garkuwa da mutane a hanyar Abuja


Wani jawabin da mai magana da yawun gwamna, Samuel Aruwan, ya saki ya nuna cewa a jiya Laraba, gwamnan ya nufi birnin tarayya Abuja sai ya isa kauyen Akilubu misalin karfe 3:40 na rana, kawai sai ya hagi tarun motoci kan hanya inda sukace masu garkuwa da mutane na kan gaba.

KU KARANTA: A karon farko Shugaba Buhari ya yi magana akan zaben Kano.

Yace: "Jami'an tsaron gwamnan sun kawar da masu garkuwa da mutanen wadanda suka arce cikin daji."
"Bayan bude hanyar, gwamna El-Rufa'i ya bada umurnin cewa wadanda yan bindigan suka jiwa rauni a kaisu asibiti da gaggawa."
"Kana gwamnan ya umurci jami'an tsaro su tsananta sintiri a hanyar domin kawar da yan barandan."

GA HOTUNAN




DUBA KUMA
Top3




You may Like the vedio? WATCH IT HERE

Wednesday

Tirkashi : Yadda el-rufa'i yayi arangama da masu garkuwa da mutane a hanyar Abuja

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufa'i ya yi arangama da masu garkuwa da mutane yayinda suke kokarin sace matafiya a hanyar Kaduna zuwa Abuja da ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2019.

El'rufa'i kaduna

Wani jawabin da mai magana da yawun gwamna, Samuel Aruwan, ya saki ya nuna cewa a ranar Laraba, gwamnan ya nufi birnin tarayya Abuja sai ya isa kauyen Akilubu misalin karfe 3:40 na rana, kawai sai ya hagi tarun motoci kan hanya inda sukace masu garkuwa da mutane na kan gaba.

KU KARANTA: A karon farko Shugaba Buhari ya yi magana akan zaben Kano.

Yace: "Jami'an tsaron gwamnan sun kawar da masu garkuwa da mutanen wadanda suka arce cikin daji."
"Bayan bude hanyar, gwamna El-Rufa'i ya bada umurnin cewa wadanda yan bindigan suka jiwa rauni a kaisu asibiti da gaggawa."
"Kana gwamnan ya umurci jami'an tsaro su tsananta sintiri a hanyar domin kawar da yan barandan."

Mun kawo muku rahoton cewa sakamakon hare-hare da garkuwa da mutanen da ya addabi babban hanyar Abuja zuwa Kaduna da kuma Kaduna zuwa Birnin gwari, majalisar tsaron jihar Kaduna ta yanke shawaran karfafa sintiri a hanyoyin domin rage hare-haren.

Masu garkuwa da mutane sun dawo hanyar Kaduna zuwa Abuja da kuma hanyar birnin gwari. Tsakanin ranar Lahadi da Litinin kadai, an yi garkuwa da akalla mutane 42.

SOURCE LEGIT.NG

Tuesday

Hattara Dai : Ana Shirin Tayar Da Fitina A Jihar Kaduna, Inji Shugaban Karamar Hukumar Sanga

A jiya Litinin ne, Shugaban Karamar Hukumar Sanga dake jihar Kaduna, Mista Charles Danladi, ya ankarar da jami’an tsaro a kan wani gaggarunmin shiri da wasu ke yi na haifar da tashin hankali a yankin.
Jigawa state governor

Mista Danladi ya bayyana haka ne a taron manema labarai da ya gabatar a garin Kaduna, inda ya kuma kara da cewa, mutanen sun yi gangami ranar Lahadi inda suka shirya tayar da tarzoma a yankin.

“Ina mai sanar da al’umma wani shiri da wasu mutane suke yi na tayar da rikicin addini a yankin karamar hukumar Sanga, ina kuma bukatar ku gaggauta kawo dauki tare da samar da cikkaken tsaro da zaman lafiya a yankin gaba daya.
“Wadanda suke wannna shirin sun yi taro a Kaduna a karkashin wata jam’iyyar siyasa a karshen mako.
“Da yammacin ranar Lahadi 31 ga watan Maris 2019 sun aika kudade karamar hukuma Sanga don ayi amfani da su wajen gudanar da zanga zangan da suka shirya yi ranar Talata 2 ga watan Afrilu 2019.
“Bayanan da muka samu yana nuna cewa, mutane na kokarin haifar da rikicin addinini ne a hanyar kawo raraba a tsakamin mutanen yankin wanda daga nan ne mataimakiyar zababbabiyar gwamna Dakta Hadiza Balarabe ta fito,“ inji Danladi.

Ya kuma kara da cewa, masu wannan shirin sun shirya watsa labaran karya na cewa, masu neman tayar da fitinan suna son yada cewa, wai mataimakiyar gwamnan na shirin sauke shugaban karamar hukumar saboda wai kirista ne.

“Babu wani labari mai kama da haka kuma masu wannan shirin na sane da hakan, amma suna yada karya ne don haifar da tashin hankali a yankin, mutane dake zaman lafiya da juna na tsawon lokaci.
“A matsayi na shugaban karamar hukumar Sanga, hakki nane na tabbatar da an samu cikakken zaman lafiya a yankin, tare da kuma kaucewa barkewar rikici a fadin karamar hukumar dama jihar gaba daya.
“A kan haka ne muke masu zama a cikin shiri don bankado dukkan wani shiri na haifar da tashin hankalin da zai iya cutar da jama’armu ta hanyar yada jita jita da karya a tsakanin al’umma,“ inji shi.

 KARANTA KUMA : Yan Boko Haram sun bankawa kauyen Chibok wuta

Duk da cewa, Danladi, bai zaiyana sunayen mutanen da ake zargin ba amma ya tabbatar wa da jama’a cewa, karamar hukumar ta yi dukkan abin da ya kamata na ganin ba a sake samun barkewar abin da ya faru a yankin Nandu ba kwanakin baya ba.


Haka kuma shugaban karamar hukumar ya ce, hukuma samar da agajin gaggawa ta jihar SEMA sun samar da kayan tallafi ga al’umma yankin Nandu bayan da aka kai masu harin.

“Karamar hukumar na kokarin gyara gidajen jama’ar da aka lalata kafin zuwa ruwan sama.

“ A kan haka muke kira ga jami’an tsaro su gagauta hukunta dukkan wadanda suke da hannu wajen shirin tayar a hankalin jama’a a fadin karamar hukumar,“ inji Danladi.

Yan Boko Haram sun bankawa kauyen Chibok wuta


Wasu yan kungiyar tada kayar bayan Boko Haram sun sake kai hari karamar hukumar Chibok dake jihar Borno, Arewa maso gabashin Najeriya. Wannan hari ya biyo bayan hare-hare da kona gidajen da yan ta'ddan suka kai kwanaki uku baya garin Gatamwarma da Chibok.
Chibok village

Wata majiya mai karfi ta bayyawana The Cable cewa an kai harin ne yayinda rundunar sojin 117 Batallion suke shirin shiga kauyen Kaumutiyahi.

Majiyar tace: "A gaskiya akwai Soji a hanyar kimanin kilomita shida da garin da aka hari, amma za su bukaci karin runduna."
Wani mazaunin Chibok ya bayyana cewa: " Sun shigo ta dajin Sambisa misalin karfe 7 na dare kuma tun lokacin suke bankawa kauyen wuta."

KU KARANTA: 'Yar Shi'a, wacce ake kashewa 'yaya 5, na shida na kwance da harasasai cikin kirjinsa, ta ce babu gudu, ba ja da baya

A watan Disamba, yan ta'addan sun kai hari kauyen Makalama dake Gatamawarwa. Sannan suka kai hari Bwalakia kwanaki uku bayan haka, inda suka kona gidajen mutane.

Daya daga cikin wanda abin ya shafa yace: "Sun sace mana dukkan abinda muke da shi kuma suka kona gidan. Bamu da abinci, bamu da wajen kwana."

KU KARANTA :  Yanzu-Yanzu :- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5 A Borno

Za ku tuna cewa a watan Nuwamban 2018, Shehun Borno, Abubakar El-Kanemi ya bayyana cewa jama'ar yankin Chibok na karkashin Boko Haram har yanzu.
A lokacin da muke kawo wannan rahoto, kakakin hukumar Soji, Sagir Musa, bai yi tsokaci kan harin ba yayinda aka tuntubeshi.

Sunday

Yanzu-Yanzu :- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5 A Borno

Dakarun gamayyar sojin MNJTF, wacce ke kula da kasashen da ke fama da hare-haren Boko Haram mai Hedikwata a birnin N’Djamena dake kasar Chadi, tare da hadin gwiwar dakarun sojin Nijeriya a Borno, sun yi nasarar hallaka wasu mayakan Boko Haram 5, sannan wasu mayakan uku suka mika wuya.
Ta'addancin boko haram

Kakakin rundunar ta MNJTF Kanal Timothy Antigha, ya ce dakarun rundunar sun hallaka mayakan na Boko Haram ne a Doron Naira da ke Borno, inda kuma uku suka mika kansu a Kamaru.

Check :- High Paying Jobs Available for You.

Kanal Antihga ya kara da cewa dakarun rundunar MNJTF sun yi nasarar kamawa tare da lalata wata mota dake yiwa mayakan na Boko Haram safarar man fetur da sauran kayayyakin da suke bukata, a tsakanin Damasak, Garunda da kuma Gazabure.

Hakazalika rundunar Sojin hadin gwiwar sun kuma kwance wasu bama-bamai uku da mayakan na Boko Haram suka binne a gefen hanya.

SAUKE TA NAN

Saturday

Da duminsa: 'Yan bindiga sun bude wuta a wurin taron biki a Kogi

A yau Asabar 30 ga watan Maris ne wasu 'yan bindiga suka tarwatsa taron bikin kamun kifi na Dankwo da ake gudanarwa duk shekara-shekara a garin Lokoja bayan sun bude wuta ga mahallarta taron.

Ta'addancin

Kamfanin dillancin labarai, NAN ta ruwaito cewa an fara bikin da misalin sa'a guda ne lokacin da 'yan bindigan suka kawo farmaki inda ake bikin a rafin Kabawa cikin kwale-kwale mai inji.

'Yan bindigan da suka taho su uku a cikin kwale-kwale mai inji sunyi ruwan harsashi a cikin taron wanda haka ya sa al'umma suka fara tserewa sai dai sun harbi mutane biyar.

DUBA WANNAN: Dalilin da yasa Kanawa suka zabi Ganduje akan Abba Gida Gida

'Yan bindiga sun bude wuta a wurin taron bikin kamun kifi a Kogi, mutane 5 sun jikkata

An sanar da jami'an 'yan sanda nan take sai dai kafin su iso wurin 'yan bindigan sun tsere a cikin kwale-kwalen da suka taho.
Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Kogi, DSP William Aya ya tabbatar da afkuwar lamarin inda ya ce abin bakin ciki ne.
A cewarsa, dukkan mutane biyar da suka jikkata suna nan da ransu suna karbar magani a cibiyar lafiya na gwamnatin tarayya da ke Lokoja.

Ya ce babu wanda ya mutu sakamakon harin kuma tuni an kama mutane biyu da ake zargi da hannu a cikin kai harin.
Aya ya ce an fara cikaken bincike a kan harin kuma za a hukunta duk wanda aka samu da hannu cikin aikata wannan mummunan lamarin.

Thursday

Harin Makiyaya ya salwantar da rayuka 10 a wata jihar Arewa

Cikin duhu a dare Kimanin rayukan mutane 10 sun salwanta a wani sabon hari na makiyaya da ya auku cikin kauyen Tse loreleegeb da ke karkashin karamar hukumar Guma a jihar Benuwe.
Ta'addanci

Shafin jaridar Vanguard ya ruwaito cewa, hukumar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da salwantar rayukan mutane biyar yayin aukuwar wannan mummuman hari cikin duhu a dare.

Rahotanni sun bayyana cewa, maharan da suka kutso daga makociyar jiha ta Nasawara a daren Talata sun yi aman wuta na harsashin bindiga kan duk wanda suka riska.

Ba ya ga kisan kiyashi da suka yiwa al'umma, maharan sun kuma kone gidaje, bukkoki, da kuma gonaki a yankin na gundumar Babai.

Majiyar jaridar Legit.ng ta ruwaito cewa, a halin yanzu al'ummar kauyen sun nemi mafaka a kauyuka na kurkusa da ke garin Daudu a sakamakon fargaba ta abinda ka iya biyo baya.

Shugaban karamar hukumar Guma, Mista Anthony Shawon, yayin tabbatar da aukuwar harin da ya salwantar da rayukan mutane goma, ya ce maharan sun kutso daga makociyar jiha da ta kasance Nasarawa.

Ya yi kira ga hukumomi masu ruwa da tsaki kan tabbatar da tsaro a yankin, da su sanya wani shamaki na tsananta bincike akan iyaka ta jihar Benuwe da kuma Nasarawa.

KARANTA KUMA: Yadda Hukumar INEC tayi min kwangen kuri'u a jihohi 31 - Atiku Ya Bayyana sakamakon zabe.

Yayin tabbatar da aukuwar hari tare da kira na tsananta tsaro, Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar, DSP Catherine Anene, ta ce kawowa yanzu bincike ya tabbatar da salwantar rayukan mutane biyar da suka riga mu gidan gaskiya.

A na sa bangaren, Kwamandan rundunar dakarun soji ma su aikin sintiri a yankunan Arewa ta Tsakiya, Janar Adeyemi Yekini, ya ce tuni bincike ya kan kama domin kwance duk wata tufka da warwara da ke tattare da aukuwar hari.

SOURCE LEGIT.NG

Monday

Da duminsa: 'Yan bindiga sun sace babban basarake a kudancin Najeriya

Punch ta ruwaito cewa wasu maza dauke da makamai wanda adadin su ya kai biyar ne su kayi kutse cikin fadar basaraken a sanyin safiyar ranar Asabar.
Yan bindiga

An ce sun ta harbe-harben harsashi a iska kafin su kayi awon gaba da Enogie zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Wata majiya daga kauyen ta ce 'yan bindigan sun bankawa motarsu wuta kafin suka tasa keyar basaraken cikin motarsa kirar Nissan Sunny suka tafi da shi.
An gano cewar sun kama hanyar jihar Delta da basaraken.


DUBA WANNAN : Hukumar 'yan sanda ta bayyana matakin da za ta dauka kan harin da aka kai jihar Kaduna


Enogie dai tsohon sufritandan 'yan sanda ne da ya gaji mahaifinsa da ya rasu wasu shekaru da suka gabata.
Kakakin yan sandan na jihar, Chidi Nwabuzor ya tabbatar da afkuwar lamarin a hirar ya yi da majiyar Legit.ng inda ya ce tuni sun fara bincike a kan lamarin.
"Eh, da gaske ne, Yan sanda sun fara bincike a kan lamarin domin tabbatar da cewa an kwato basaraken cikin koshin lafiya," inji shi.

Sunday

Hukumar 'yan sanda ta bayyana matakin da za ta dauka kan harin da aka kai jihar Kaduna

Hukumar rundunar 'yan sandan jihar Kaduna, a yau Lahadi, ta sha alwashin damko wadanda suka kai hari kauyen Nandu da ke karkashin karamar hukumar Sanga ta jihar domin su fuskanci hukunci daidai da abinda suka aikata.
"Yan sanda

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, DSP Yakubu Sabo, shi ne ya bayar da shaidar hakan yayin ganawa da manema labarai na kamfanin dillancin labarai na kasa a yau Lahadi cikin birnin Kaduna.

DSP Sabo ya bayar da shaidar cewa, hukumar 'yan sandan jihar ta gindaya jami'an tsaro sako-sako a yankunan da wannan ta'addancin ya auku inda a halin yanzu tuni sun killace gawawwakin wadanda suka riga mu gidan gaskiya tare da mika wadanda suka jikkata zuwa Asibiti.

Babban jami'in dan sandan ya bayyana cewa, rundunar 'yan sanda tare da hadin gwiwar dakarun sojin kasa sun bazama a yakin da wannan mummunan ibtila'i ya auku domin tabbatar da kiyaye doka da kuma kwantar da tarzoma.

Yayin tur gami da Allah wadai dangane da aukuwar wannan annoba, kwamishinan 'yan sanda na jihar, CP Ahmed Abdurrahman ya jajanta tare a mika sakonnin sa na gaisuwa da kuma ta'aziyya ga 'yan uwan wadanda da tsautsayin ya ritsa da su.

A cewar DSP Sabo, Kwamishinan na 'yan sandan ya gargadi al'ummar yankin Nandu da su kauracewa daukar hukuncin doka a hannayen su tare da shawartar su kan sanya idanun lura dangane da yadda hukunci na shari'a zai dauki mataki.

Jaridar Legit.ng ta ruwaito cewa, a jiya Asabar, 16 ga watan Maris na 2019, 'yan bindiga dadi suka harbe mutane 9 har Lahira tare da raunata mutane biyu gami da kone mahallan mazauna kauyen Nandu da ke karamar hukumar Sanga a jihar Kaduna.

SOURCE LEGIT.NG

Friday

Yanzu yanzu: An saki surukar Gwamna Masari da aka yi garkuwa da ita

Surukar Gwamna Aminu Masari, Hajiya Hauwa Yusuf ta dawo gida bayan wadanda suka sace ta sun sako ta bayan shafe kwanaki 8 da ta yi a hannun su.
Aminu bello masari

Kakakin rundunan yan sanda reshen Katsina, SP Gambo Isah yace an sako ta cikin koshin lafiya sannan kuma a halin yanzu ta koma ga yan uwanta bayan gwaje gwaje da aka kammala.

NNPC requirements 2019 Open on careers.nnpcgroup.com

Ku tuna a baya cewa rundunan yan sanda tace suna bin duddugin wani wanda ake zargin yana da hannu cikin lamarin.
Anyi garkuwa da Hajiya Yusuf ne a Gidan ta dake a Dundume Crescent a Katsina, a ranar juma’a da ya gabata.

DUBA WANNAN : N400 Per Refferal, No Payment Needed - Try it